Wasu ’yan bindiga sun yi garkuwa da Dagacin ƙauyen Aujarawar Alkali da ke Ƙaramar Hukumar Gezawa a Jihar Kano, Alhaji Ahmad Yakubu Ahmad.
Lamarin ya faru ne a daren Alhamis, 17 ga Satumba, 2026, lokacin da maharan ɗauke da manyan makamai suka shiga ƙauyen, suka yi awon gaba da dagacin zuwa wani wurin da ba a san inda yake ba.
Mahi Isma’il, mai magana da yawun Zannan Kano kuma Dagacin Jogana, ya tabbatar da sace dagacin a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a. Ya ce lamarin ya faru ne a Aujarawar Alkali, yayin da mazauna yankin suka bayyana cewa maharan sun zo ɗauke da muggan makamai.
Bayan faruwar lamarin, an yi kira ga jami’an tsaro da su ƙara ƙaimi wajen ceto dagacin tare da ƙarfafa kasancewar jami’an tsaro a yankunan karkara na jihar. An kuma buƙaci mazauna yankin su kwantar da hankulansu, su kasance masu taka-tsantsan tare da bai wa jami’an tsaro haɗin kai domin tabbatar da dawowar dagacin cikin ƙoshin lafiya.
Rahoton KanoTimes ya bayyana cewa; Rundunar ƴannandan Jihar Kano ba ta fitar da sanarwa kan lamarin ba. Haka kuma, babu wani bayani da aka tabbatar kan inda dagacin yake ko kuma ko an samu nasarar ceto shi.














