An samu gagarumin sauyin sheƙa a jam’iyyun APC, NNPP, da PDP a Jihar Jigawa, inda ‘yan siyasa da magoya bayansu suka koma jam’iyyar ADC.
A ranar Lahadi, A Dutse, babban birnin Jihar Jigawa, ya shaida taron jama’a mai yawa na magoya baya da ‘yan siyasa yayin wani babban taro da aka shirya domin karɓar tsohon sanata mai wa’adi biyu da ya wakilci mazabar Jigawa ta Kudu maso Yamma, Sanata Sabo Nakudu, wanda ya sauya sheka zuwa ADC tare da sauran magoya bayansa.
- Shugaba Tinubu Ya Amince Da Biyan Naira Tiriliyan 3.3 Domin Warware Bashin Wutar Lantarki
- Sojoji Sun Kwato Yankuna, Sun Kashe Ƴan Bindiga 65 A Zamfara
Nakudu, tare da wasu ‘yan siyasa daga sassa daban-daban na jihar, sun samu kyakkyawar tarba daga shugabannin ADC.
Tsohon sanatan, wanda ya jagoranci kwamitin Majalisar Dattawa kan harkokin man fetur a majalisa ta 9, ya yi murabus daga APC a ranar Juma’a sannan ya shiga ADC a ranar Lahadi.
Da yake magana bayan karɓar katin zama ɗan jam’iyyar ADC, Nakudu ya ce, “Ina godiya ga magoya bayana bisa fitowa da yawa domin tarbata zuwa sabuwar jam’iyyata,” ya ƙara da cewa, “Na yi alƙawarin yin aiki domin ganin an samar da cigaba mai ɗorewa a Jigawa da ma ƙasa baki ɗaya.”
Ana sa ran Nakudu, wanda ya fafata da Gwamna Umar Namadi a zaɓen fidda gwani na gwamna na APC a shekarar 2023, zai sake tsayawa takarar gwamna a ƙarƙashin tutar ADC a shekarar 2027.















Discussion about this post