ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kwato Yankuna, Sun Kashe Ƴan Bindiga 65 A Zamfara

by Abubakar Sulaiman
3 months ago
Zamfara

Dakarun Operation FANSAR YAMMA sun samu gagarumar nasara a yaƙi da ‘yan bindiga a jihar Zamfara, inda suka kashe aƙalla ‘yan bindiga 65 ciki har da ɗan wani fitaccen jagoran ‘yan bindiga da ake nema ruwa a jallo, a wani zazzafan farmaki da aka kai ta ƙasa da sama a ƙaramar hukumar Tsafe.

Rahotanni sun nuna cewa harin ya auku ne a ƙauyen Munhaye da ke bayan Kunchin Kalgo, inda aka kashe Kachalla Iliya Sarki, wanda ke daga cikin manyan kwamandojin ƙungiyar kuma ɗan Ado Allero, tare da wasu manyan jagorori irin su Dogo Sule da Iliya Mai Rasha, waɗanda ake zargi da hannu a hare-hare da garkuwa da mutane a yankin Arewa maso Yamma.

  • Motoci 3 Masu Amfani Da Gas (CNG) Sun Yi Bindiga A Tashar Mota A Kaduna
  • Gwamna Bago, Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Bindiga Da Masu Ba Su Bayanai

Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa an fara gumurzu mai tsanani ne da misalin ƙarfe 6:00 na yammacin ranar Asabar, 4 ga Afrilu, 2026, inda ɗaruruwan ‘yan bindiga ɗauke da makamai suka kai hari da babura kusan 300 daga yankunan Yan Wari da sansanin Dankarami Gwaska, amma dakarun sojoji tare da taimakon hare-haren jiragen sama suka daƙile su bayan shafe sama da sa’o’i bakwai ana musayar wuta.

ADVERTISEMENT

Sai dai duk da wannan nasara, an yi asarar rayukan wasu jami’an ‘yan sa-kai guda bakwai da suka taimaka wa sojojin a fafatawar, yayin da rahotanni ke cewa Ado Allero ya tsere daga yankin zuwa garin Yankuzu, inda ake zargin yana ɓoye, yayin da sojoji ke ci gaba da farautarsa da sauran mabiyansa domin murƙushe su gaba ɗaya.

Masana harkokin tsaro sun bayyana kashe Iliya Sarki a matsayin babbar koma baya ga ‘yan bindiga a yankin, suna mai cewa hakan zai raunana tsarin jagoranci da ayyukan ƙungiyar, sai dai sun yi gargadin cewa hakan na iya haifar da ramuwar gayya, don haka an sanya jami’an tsaro cikin shirin ko-ta-kwana a yankunan da ke cikin haɗari yayin da ake ci gaba da aikin share yankunan daga ragowar ‘yan bindigar.

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

Zamfara
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata
  • Abubakar Sulaiman
    Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Labarai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
'yansanda
Labarai

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Next Post
Kasar Sin Za Ta Hada Hannu Da Kasar Rasha Wajen Yayyafawa Rikicin Gabas Ta Tsakiya Ruwan Sanyi

Kasar Sin Za Ta Hada Hannu Da Kasar Rasha Wajen Yayyafawa Rikicin Gabas Ta Tsakiya Ruwan Sanyi

LABARAI MASU NASABA

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.