ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kwato Yankuna, Sun Kashe Ƴan Bindiga 65 A Zamfara

by Abubakar Sulaiman
5 months ago
Zamfara

Dakarun Operation FANSAR YAMMA sun samu gagarumar nasara a yaƙi da ‘yan bindiga a jihar Zamfara, inda suka kashe aƙalla ‘yan bindiga 65 ciki har da ɗan wani fitaccen jagoran ‘yan bindiga da ake nema ruwa a jallo, a wani zazzafan farmaki da aka kai ta ƙasa da sama a ƙaramar hukumar Tsafe.

Rahotanni sun nuna cewa harin ya auku ne a ƙauyen Munhaye da ke bayan Kunchin Kalgo, inda aka kashe Kachalla Iliya Sarki, wanda ke daga cikin manyan kwamandojin ƙungiyar kuma ɗan Ado Allero, tare da wasu manyan jagorori irin su Dogo Sule da Iliya Mai Rasha, waɗanda ake zargi da hannu a hare-hare da garkuwa da mutane a yankin Arewa maso Yamma.

  • Motoci 3 Masu Amfani Da Gas (CNG) Sun Yi Bindiga A Tashar Mota A Kaduna
  • Gwamna Bago, Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Bindiga Da Masu Ba Su Bayanai

Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa an fara gumurzu mai tsanani ne da misalin ƙarfe 6:00 na yammacin ranar Asabar, 4 ga Afrilu, 2026, inda ɗaruruwan ‘yan bindiga ɗauke da makamai suka kai hari da babura kusan 300 daga yankunan Yan Wari da sansanin Dankarami Gwaska, amma dakarun sojoji tare da taimakon hare-haren jiragen sama suka daƙile su bayan shafe sama da sa’o’i bakwai ana musayar wuta.

ADVERTISEMENT

Sai dai duk da wannan nasara, an yi asarar rayukan wasu jami’an ‘yan sa-kai guda bakwai da suka taimaka wa sojojin a fafatawar, yayin da rahotanni ke cewa Ado Allero ya tsere daga yankin zuwa garin Yankuzu, inda ake zargin yana ɓoye, yayin da sojoji ke ci gaba da farautarsa da sauran mabiyansa domin murƙushe su gaba ɗaya.

Masana harkokin tsaro sun bayyana kashe Iliya Sarki a matsayin babbar koma baya ga ‘yan bindiga a yankin, suna mai cewa hakan zai raunana tsarin jagoranci da ayyukan ƙungiyar, sai dai sun yi gargadin cewa hakan na iya haifar da ramuwar gayya, don haka an sanya jami’an tsaro cikin shirin ko-ta-kwana a yankunan da ke cikin haɗari yayin da ake ci gaba da aikin share yankunan daga ragowar ‘yan bindigar.

LABARAI MASU NASABA

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Zamfara
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Rahotonni

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara
Labarai

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia
Manyan Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
Next Post
Kasar Sin Za Ta Hada Hannu Da Kasar Rasha Wajen Yayyafawa Rikicin Gabas Ta Tsakiya Ruwan Sanyi

Kasar Sin Za Ta Hada Hannu Da Kasar Rasha Wajen Yayyafawa Rikicin Gabas Ta Tsakiya Ruwan Sanyi

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.