ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wanene Alhaji Ibrahim Galadima Tsohon Shugaban Hukumar Kwallon Kafar Nijeriya

by Rabilu Sanusi Bena
2 months ago

Magoya bayan kwallon kafa a Nijeriya na cigaba da jimamin rashin daya daga cikin fitattun mutane a fagen kwallon kafa a Nijeriya, Alhaji Ibrahim Galadima, tsohon shugaban hukumar kwallon kafa ta Nijeriya (NFA), wadda yanzu aka fi sani da (NFF), Alhaji Galadima ya rasu a ranar Asabar, 18 ga watan Afrilun shekarar 2026, a Kano, yana da shekaru 74.

Alhaji Sani Ahmed Toro, tsohon Sakatare Janar na hukumar NFA, wanda ya yi aiki tare da Galadima a lokacin baya ne ya tabbatar da labarin rasuwarsa, Toro, a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce, “Ina matukar bakin ciki da sanar da mutuwar Alh Ibrahim Galadima, tsohon Shugaban NFA, a yau a Kano, Allah ya saka masa da Aljanna Firdausi”.

  • Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

An haifi Alhaji Galadima a ranar 14 ga watan Yunin 1951, a karamar hukumar Fagge dake Kano, ya shafe muhimmin lokacin rayuwarsa wajen ganin ci gaban wasanni a Nijeriya, musamman kwallon kafa, ya shugabanci hukumar kwallon kafa ta jihar jihar Kano tsakanin shekarun 1977 da 1979, ya cigaba da aikinsa a ma’aikatar wasanni bayan ya zama shugaban Gudanarwa na Majalisar Wasanni ta Jihar Kano daga shekarar 1981 zuwa 1983.

ADVERTISEMENT

Gwamnatin tarayya a wancan lokacin ta bukaci yayi aiki da ita a matakin kasa, wanda hakan ya sa aka nada shi memba na Kwamitin Kula da Wasanni na Hukumar Wasanni ta kasa a shekarar 1983, tasirin Galadima ba a iya kwallon kafa kawai ta tsaya ba bayan ya zama mataimakin shugaban kwamitin Olympics na Nijeriya (NOC) a shekarar 1985, kujerar da ya rike har zuwa shekarar 1987.

Galadima ya taba zama Kwamishinan Jin Daɗin Jama’a, Matasa da Wasanni a shekarar 1989, daga baya kuma ya zama Kwamishinan Ayyuka, Gidaje da Sufuri, ya kuma kasance memba na Kwamitin Kula da Shugaban Kasa kan bunkasa filayen wasa na Gasar Cin Kofin Matasan Duniya ta FIFA da Nijeriya ta karbi bakunci a shekarar 1995, gasar da daga karshe aka mayar da ita Qatar saboda barkewar cutar sankarau a wani yanki na Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Alhaji Galadima ya sake zama memba na Kwamitin Gasar Matasa na CAF. A shekarar 1999, ya taka muhimmiyar rawa a lokacin da ya rike shugaban kwamitin wasanni na jihar Kano a Gasar Cin Kofin Matasa ta FIFA a Nijeriya a shekarar 1999, babbar nasarar da ya samu a harkokin kwallon kafa ta zo ne a shekarar 2002 lokacin da aka zabe shi Shugaban hukumar Kwallon Kafa ta Nijeriya a wancan lokacin.

Ya jagoranci hukumar har zuwa shekarar 2006, inda ya bar tarihi mai kyau a tsawon shekaru 4 da yayi a saman kujerar, bayan rawar da ya taka a matakin kasa, ya kuma koma Kano domin yin aiki a matsayin shugaban Kungiyar Kwallon Kafa ta Kano Pillars, daga baya kuma ya zama shugaban Hukumar Wasanni ta Jihar Kano, wanda hakan ya sake tabbatar da matsayinsa a matsayin babban mutum a bangaren wasanni a Nijeriya, mutuwar Alhaji Ibrahim Galadima ta bar wani babban gibi a harkar kwallon kafa ta Nijeriya wanda za a shafe tsawon lokaci ana tunawa dashi, amma kuma tarihin da ya bari ba zai taba goguwa a zukatan masoya harkar kwallon kafa a kasar ba.

Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Mutum-Mutumin Inji Na Sin Ya Cimma Saurin Dan Adam A Gasar Tseren Rabin Dogon Zango

Mutum-Mutumin Inji Na Sin Ya Cimma Saurin Dan Adam A Gasar Tseren Rabin Dogon Zango

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.