ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wanene Alhaji Ibrahim Galadima Tsohon Shugaban Hukumar Kwallon Kafar Nijeriya

by Rabilu Sanusi Bena
3 months ago

Magoya bayan kwallon kafa a Nijeriya na cigaba da jimamin rashin daya daga cikin fitattun mutane a fagen kwallon kafa a Nijeriya, Alhaji Ibrahim Galadima, tsohon shugaban hukumar kwallon kafa ta Nijeriya (NFA), wadda yanzu aka fi sani da (NFF), Alhaji Galadima ya rasu a ranar Asabar, 18 ga watan Afrilun shekarar 2026, a Kano, yana da shekaru 74.

Alhaji Sani Ahmed Toro, tsohon Sakatare Janar na hukumar NFA, wanda ya yi aiki tare da Galadima a lokacin baya ne ya tabbatar da labarin rasuwarsa, Toro, a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce, “Ina matukar bakin ciki da sanar da mutuwar Alh Ibrahim Galadima, tsohon Shugaban NFA, a yau a Kano, Allah ya saka masa da Aljanna Firdausi”.

  • M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa
  • Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
  • Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
  • Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya
  • Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

An haifi Alhaji Galadima a ranar 14 ga watan Yunin 1951, a karamar hukumar Fagge dake Kano, ya shafe muhimmin lokacin rayuwarsa wajen ganin ci gaban wasanni a Nijeriya, musamman kwallon kafa, ya shugabanci hukumar kwallon kafa ta jihar jihar Kano tsakanin shekarun 1977 da 1979, ya cigaba da aikinsa a ma’aikatar wasanni bayan ya zama shugaban Gudanarwa na Majalisar Wasanni ta Jihar Kano daga shekarar 1981 zuwa 1983.

ADVERTISEMENT

Gwamnatin tarayya a wancan lokacin ta bukaci yayi aiki da ita a matakin kasa, wanda hakan ya sa aka nada shi memba na Kwamitin Kula da Wasanni na Hukumar Wasanni ta kasa a shekarar 1983, tasirin Galadima ba a iya kwallon kafa kawai ta tsaya ba bayan ya zama mataimakin shugaban kwamitin Olympics na Nijeriya (NOC) a shekarar 1985, kujerar da ya rike har zuwa shekarar 1987.

Galadima ya taba zama Kwamishinan Jin Daɗin Jama’a, Matasa da Wasanni a shekarar 1989, daga baya kuma ya zama Kwamishinan Ayyuka, Gidaje da Sufuri, ya kuma kasance memba na Kwamitin Kula da Shugaban Kasa kan bunkasa filayen wasa na Gasar Cin Kofin Matasan Duniya ta FIFA da Nijeriya ta karbi bakunci a shekarar 1995, gasar da daga karshe aka mayar da ita Qatar saboda barkewar cutar sankarau a wani yanki na Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Alhaji Galadima ya sake zama memba na Kwamitin Gasar Matasa na CAF. A shekarar 1999, ya taka muhimmiyar rawa a lokacin da ya rike shugaban kwamitin wasanni na jihar Kano a Gasar Cin Kofin Matasa ta FIFA a Nijeriya a shekarar 1999, babbar nasarar da ya samu a harkokin kwallon kafa ta zo ne a shekarar 2002 lokacin da aka zabe shi Shugaban hukumar Kwallon Kafa ta Nijeriya a wancan lokacin.

Ya jagoranci hukumar har zuwa shekarar 2006, inda ya bar tarihi mai kyau a tsawon shekaru 4 da yayi a saman kujerar, bayan rawar da ya taka a matakin kasa, ya kuma koma Kano domin yin aiki a matsayin shugaban Kungiyar Kwallon Kafa ta Kano Pillars, daga baya kuma ya zama shugaban Hukumar Wasanni ta Jihar Kano, wanda hakan ya sake tabbatar da matsayinsa a matsayin babban mutum a bangaren wasanni a Nijeriya, mutuwar Alhaji Ibrahim Galadima ta bar wani babban gibi a harkar kwallon kafa ta Nijeriya wanda za a shafe tsawon lokaci ana tunawa dashi, amma kuma tarihin da ya bari ba zai taba goguwa a zukatan masoya harkar kwallon kafa a kasar ba.

Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Kofin Duniya: Na fi Son Faransa Ta Kara Da Argentina A Wasan Ƙarshe A Kan Ingila — Vieira

MASU ALAKA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Next Post
Mutum-Mutumin Inji Na Sin Ya Cimma Saurin Dan Adam A Gasar Tseren Rabin Dogon Zango

Mutum-Mutumin Inji Na Sin Ya Cimma Saurin Dan Adam A Gasar Tseren Rabin Dogon Zango

LABARAI MASU NASABA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.