ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wanene Alhaji Ibrahim Galadima Tsohon Shugaban Hukumar Kwallon Kafar Nijeriya

by Rabilu Sanusi Bena
2 months ago

Magoya bayan kwallon kafa a Nijeriya na cigaba da jimamin rashin daya daga cikin fitattun mutane a fagen kwallon kafa a Nijeriya, Alhaji Ibrahim Galadima, tsohon shugaban hukumar kwallon kafa ta Nijeriya (NFA), wadda yanzu aka fi sani da (NFF), Alhaji Galadima ya rasu a ranar Asabar, 18 ga watan Afrilun shekarar 2026, a Kano, yana da shekaru 74.

Alhaji Sani Ahmed Toro, tsohon Sakatare Janar na hukumar NFA, wanda ya yi aiki tare da Galadima a lokacin baya ne ya tabbatar da labarin rasuwarsa, Toro, a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce, “Ina matukar bakin ciki da sanar da mutuwar Alh Ibrahim Galadima, tsohon Shugaban NFA, a yau a Kano, Allah ya saka masa da Aljanna Firdausi”.

  • Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

An haifi Alhaji Galadima a ranar 14 ga watan Yunin 1951, a karamar hukumar Fagge dake Kano, ya shafe muhimmin lokacin rayuwarsa wajen ganin ci gaban wasanni a Nijeriya, musamman kwallon kafa, ya shugabanci hukumar kwallon kafa ta jihar jihar Kano tsakanin shekarun 1977 da 1979, ya cigaba da aikinsa a ma’aikatar wasanni bayan ya zama shugaban Gudanarwa na Majalisar Wasanni ta Jihar Kano daga shekarar 1981 zuwa 1983.

ADVERTISEMENT

Gwamnatin tarayya a wancan lokacin ta bukaci yayi aiki da ita a matakin kasa, wanda hakan ya sa aka nada shi memba na Kwamitin Kula da Wasanni na Hukumar Wasanni ta kasa a shekarar 1983, tasirin Galadima ba a iya kwallon kafa kawai ta tsaya ba bayan ya zama mataimakin shugaban kwamitin Olympics na Nijeriya (NOC) a shekarar 1985, kujerar da ya rike har zuwa shekarar 1987.

Galadima ya taba zama Kwamishinan Jin Daɗin Jama’a, Matasa da Wasanni a shekarar 1989, daga baya kuma ya zama Kwamishinan Ayyuka, Gidaje da Sufuri, ya kuma kasance memba na Kwamitin Kula da Shugaban Kasa kan bunkasa filayen wasa na Gasar Cin Kofin Matasan Duniya ta FIFA da Nijeriya ta karbi bakunci a shekarar 1995, gasar da daga karshe aka mayar da ita Qatar saboda barkewar cutar sankarau a wani yanki na Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Alhaji Galadima ya sake zama memba na Kwamitin Gasar Matasa na CAF. A shekarar 1999, ya taka muhimmiyar rawa a lokacin da ya rike shugaban kwamitin wasanni na jihar Kano a Gasar Cin Kofin Matasa ta FIFA a Nijeriya a shekarar 1999, babbar nasarar da ya samu a harkokin kwallon kafa ta zo ne a shekarar 2002 lokacin da aka zabe shi Shugaban hukumar Kwallon Kafa ta Nijeriya a wancan lokacin.

Ya jagoranci hukumar har zuwa shekarar 2006, inda ya bar tarihi mai kyau a tsawon shekaru 4 da yayi a saman kujerar, bayan rawar da ya taka a matakin kasa, ya kuma koma Kano domin yin aiki a matsayin shugaban Kungiyar Kwallon Kafa ta Kano Pillars, daga baya kuma ya zama shugaban Hukumar Wasanni ta Jihar Kano, wanda hakan ya sake tabbatar da matsayinsa a matsayin babban mutum a bangaren wasanni a Nijeriya, mutuwar Alhaji Ibrahim Galadima ta bar wani babban gibi a harkar kwallon kafa ta Nijeriya wanda za a shafe tsawon lokaci ana tunawa dashi, amma kuma tarihin da ya bari ba zai taba goguwa a zukatan masoya harkar kwallon kafa a kasar ba.

Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Barcelona Ta Kammala Daukar Anthony Gordon Daga Newcastle

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Mutum-Mutumin Inji Na Sin Ya Cimma Saurin Dan Adam A Gasar Tseren Rabin Dogon Zango

Mutum-Mutumin Inji Na Sin Ya Cimma Saurin Dan Adam A Gasar Tseren Rabin Dogon Zango

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.