Magoya bayan kwallon kafa a Nijeriya na cigaba da jimamin rashin daya daga cikin fitattun mutane a fagen kwallon kafa a Nijeriya, Alhaji Ibrahim Galadima, tsohon shugaban hukumar kwallon kafa ta Nijeriya (NFA), wadda yanzu aka fi sani da (NFF), Alhaji Galadima ya rasu a ranar Asabar, 18 ga watan Afrilun shekarar 2026, a Kano, yana da shekaru 74.
Alhaji Sani Ahmed Toro, tsohon Sakatare Janar na hukumar NFA, wanda ya yi aiki tare da Galadima a lokacin baya ne ya tabbatar da labarin rasuwarsa, Toro, a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce, “Ina matukar bakin ciki da sanar da mutuwar Alh Ibrahim Galadima, tsohon Shugaban NFA, a yau a Kano, Allah ya saka masa da Aljanna Firdausi”.
- Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
- Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
- Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
- ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP
- An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
An haifi Alhaji Galadima a ranar 14 ga watan Yunin 1951, a karamar hukumar Fagge dake Kano, ya shafe muhimmin lokacin rayuwarsa wajen ganin ci gaban wasanni a Nijeriya, musamman kwallon kafa, ya shugabanci hukumar kwallon kafa ta jihar jihar Kano tsakanin shekarun 1977 da 1979, ya cigaba da aikinsa a ma’aikatar wasanni bayan ya zama shugaban Gudanarwa na Majalisar Wasanni ta Jihar Kano daga shekarar 1981 zuwa 1983.
Gwamnatin tarayya a wancan lokacin ta bukaci yayi aiki da ita a matakin kasa, wanda hakan ya sa aka nada shi memba na Kwamitin Kula da Wasanni na Hukumar Wasanni ta kasa a shekarar 1983, tasirin Galadima ba a iya kwallon kafa kawai ta tsaya ba bayan ya zama mataimakin shugaban kwamitin Olympics na Nijeriya (NOC) a shekarar 1985, kujerar da ya rike har zuwa shekarar 1987.
Galadima ya taba zama Kwamishinan Jin Daɗin Jama’a, Matasa da Wasanni a shekarar 1989, daga baya kuma ya zama Kwamishinan Ayyuka, Gidaje da Sufuri, ya kuma kasance memba na Kwamitin Kula da Shugaban Kasa kan bunkasa filayen wasa na Gasar Cin Kofin Matasan Duniya ta FIFA da Nijeriya ta karbi bakunci a shekarar 1995, gasar da daga karshe aka mayar da ita Qatar saboda barkewar cutar sankarau a wani yanki na Nijeriya.
Alhaji Galadima ya sake zama memba na Kwamitin Gasar Matasa na CAF. A shekarar 1999, ya taka muhimmiyar rawa a lokacin da ya rike shugaban kwamitin wasanni na jihar Kano a Gasar Cin Kofin Matasa ta FIFA a Nijeriya a shekarar 1999, babbar nasarar da ya samu a harkokin kwallon kafa ta zo ne a shekarar 2002 lokacin da aka zabe shi Shugaban hukumar Kwallon Kafa ta Nijeriya a wancan lokacin.
Ya jagoranci hukumar har zuwa shekarar 2006, inda ya bar tarihi mai kyau a tsawon shekaru 4 da yayi a saman kujerar, bayan rawar da ya taka a matakin kasa, ya kuma koma Kano domin yin aiki a matsayin shugaban Kungiyar Kwallon Kafa ta Kano Pillars, daga baya kuma ya zama shugaban Hukumar Wasanni ta Jihar Kano, wanda hakan ya sake tabbatar da matsayinsa a matsayin babban mutum a bangaren wasanni a Nijeriya, mutuwar Alhaji Ibrahim Galadima ta bar wani babban gibi a harkar kwallon kafa ta Nijeriya wanda za a shafe tsawon lokaci ana tunawa dashi, amma kuma tarihin da ya bari ba zai taba goguwa a zukatan masoya harkar kwallon kafa a kasar ba.















Discussion about this post