Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta musanta zargin jam’iyyar Nigeria Democratic Congress (NDC) cewa ta sauya sunayen ’yan takarar da jam’iyyar ta gabatar da wasu sunaye gabanin zaɓen 2027.
A cikin wata sanarwa da Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Masu Zaɓe na INEC, Mohammed Kudu Haruna, ya sanya wa hannu, hukumar ta bayyana zargin a matsayin “mara tushe.”
INEC ta ce jam’iyyun siyasa ne ke da alhakin zaɓa da gabatar da sunayen ’yan takararsu, yayin da aikin hukumar ya taƙaita ne wajen sa ido kan tsarin.
Hukumar ta ce dukkanin jam’iyyu 22 da suka yi rajista domin shiga zaɓen 2027 sun horar da jami’ai da za su kula da tsarin gabatar da ’yan takara, sannan aka bai wa shugabannin jam’iyyun damar shiga tsarin gabatar da sunayen.
INEC ta kuma ce jerin sunayen ’yan takarar an samar da su ne daga bayanan da shugabannin jam’iyyun suka gabatar tare da sanya hannu.
Hukumar ta ce tana da kwafin takardun da suka dace da ke nuna cewa NDC ce ta gabatar da sunayen ’yan takarar.
Saboda haka, INEC ta yi watsi da zargin cewa ita ce ta shigar ko sauya bayanan ’yan takarar jam’iyyar.
Hukumar ta tabbatar wa jam’iyyun siyasa da sauran masu ruwa da tsaki cewa za ta ci gaba da tabbatar da gaskiya, riƙon amana da gudanar da sahihin zaɓe.














