Ɗan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya ce tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, zai kasance cikakken abokin tafiya a gwamnati idan suka lashe zaɓen shugaban kasa na shekarar 2027.
Obi ya bayyana hakan ne yayin gabatar da Kwankwaso a matsayin abokin takararsa a babban taron jam’iyyar NDC da aka gudanar a Abuja.
Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party a zaben 2023 ya ce gwamnatinsu za ta kasance bisa tuntuɓar juna, haɗa kai da raba nauyin jagoranci tare, yana mai jaddada cewa ofishin mataimakin shugaban kasa ba zai zama kamar safaya ba.
A cewarsa, gwamnatin da suke son kafawa za ta bambanta da yadda ake kallon mataimakin shugaban kasa a matsayin “safaya taya.”
Obi ya ce, “Gwamnatin da muke son kafawa ba za ta kasance gwamnati irin wadda ake cewa mataimakin shugaban kasa kamar safaya taya ne.
“Mataimakin shugaban kasa zai kasance cikakken abokin tafiya saboda muna son gina kasa inda mutane biyu masu daidaito za su yi aiki domin daukakar kasa.
“Za a rika yanke shawara tare a matsayin abokan aiki. Za a tuntubi kowa. Wannan shi ne abin da muke bukata, kuma haka gwamnati ke aiki.”















Discussion about this post