Ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC a Jihar Gombe, Jamil Isiyaka Gwamna, ya yi kira ga ‘yan jam’iyyar da su haɗa kai gabanin babban zaɓen 2027.
Gwamna ya yi wannan kira ne a daidai lokacin da ake samun rashin jin daɗi a cikin jam’iyyar sakamakon tsarin sulhu na fidda gwani da ya ba shi tikitin takara.
“Bari in yi amfani da wannan dama in kira ga dukkan ‘yan jam’iyyarmu ta APC—wadanda suka yi takara da kuma wadanda suka goyi bayan ‘yan takara daban-daban—da mu haɗa kai mu zama tsintsiya madaurinki ɗaya,” in ji shi yayin ganawa da manema labarai.
Ya jaddada cewa haɗin kai yana da matuƙar muhimmanci ga nasarar jam’iyyar, yana mai cewa dole ne APC ta yi aiki tare domin samun nasara a dukkan matakan zaɓe.
A cewarsa, jam’iyyar na da damar lashe zaɓen shugaban ƙasa, na gwamna, na majalisar dattawa, na majalisar wakilai da kuma na majalisun jihohi idan aka samu cikakken haɗin kai.
“Ina da kyakkyawan fata cewa za mu cimma wannan buri, amma muna buƙatar haɗin kai,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa, “Mulki a hannun Allah yake, Shi ke ba wanda Ya so, a lokacin da Ya so, kuma yadda Ya ga dama.”















Discussion about this post