Jam’iyyar NDC ta bayyana aniyarta na tsayar da ‘yan takara masu inganci da nagarta domin tunkarar babban zaɓen 2027.
Rahotanni sun nuna cewa shugabannin jam’iyyar a Jihar Cross River ne suka bayyana hakan, inda suka jaddada cewa za su fifita gaskiya, ƙwarewa da amana wajen zaɓen ‘yan takara domin samun amincewar jama’a.
Jam’iyyar ta ce manufarta ita ce samar da ‘yan takara da za su iya kawo sauyi mai ma’ana a shugabanci, tare da magance matsalolin tattalin arziki da zamantakewa da ke addabar ƙasar.
Haka kuma, NDC ta bayyana cewa tana ƙoƙarin ƙarfafa tsarinta da haɗa kan mambobinta a matakai daban-daban, domin zama babbar madadin siyasa ga ‘yan Nijeriya gabanin zaɓen da ke tafe.
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da sabbin ƙungiyoyi da jam’iyyun siyasa ke ƙoƙarin jan hankalin masu zaɓe tare da tsara dabarun fafatawa da manyan jam’iyyun ƙasar a 2027.















Discussion about this post