ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Rashin Hadin Kan ‘Yan Adawa Ya Ba Tinubu Tazarce A Cikin Sauki —Ahmad Zangina

by Sulaiman
2 months ago
zangina

Ahamad Sani Zangina matashin dan siyasa ne kuma mai fafutukar kare hakkin al’umma. Yana kuma daga cikin wadanda suka amince da tafiyar jagorancin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu. A tattaunawarsa da Editanmu Bello Hamza a ofishinsa da ke Abuja, ya bayyana yadda rikici da kwadayin mulki na ‘yan adawa zai tallafa wa Shugaba Tinubu yin tazarce a cikin sauki. Ga dai yadda hirar ta kasance.:

Da farko za mu so ka gabatar mana da kanka.

Da farko dai sunana Ahmad Sani Zangina, dan Nijeriya mai yi wa kasa fatan Alhairi

ADVERTISEMENT

A yayin da sararin siyasar Nijeriya ta turnuke, ya kake ganin yiyuwar samun nasarar Shugaba Tinubu a zaben 2027.

Wato yadda ‘yan adawa suke tafiyar da harkokin kalubalantar gwamnatin Tinubu tamkar suna kara bashi damar lashe zabe ne ta hanyar yin tazarce a cikin sauki, saboda jam’iyyun adawar sun kasa daidaita kansu saboda kwadayin Mulki ya mamaye zukatansu ba wai kishin kasa ko talakawa suke yi ba. Haka ya hana su kafa jam’iyya daya dilo da za su yi adawa a ciki, saboda haka wannan dambarwar da suke yi yana bai wa Shugaba Tinubu damar yin tazarce kai tsaye ba tare da wata matsala ba, hakan kuma yana yi mana dadi.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Gangamin ‘yan adawar baya baku tsoro?

Lallai babu wani dan jam‘iyyar APC ko wani masaoyin Tinubu da wannan taron ‘yan adawar zai  bashi tsoro, musamman ganin yadda manyan ‘yan adawar kamar su Obi da Kwankwaso suka ware daga tafiyar ‘yan adawa, hatta ‘ya’yan shugaban ‘yan adawar Atiku Abubakar da yawa duk sun koma wajen tafiyar Shugaba Tinubu, ashe kaga ya kamata dukkanmu muna mu kwashe inamu inamu mu koma wajen Tinubu don ganin ya samu nasara a zaben da ke tafe domin ci gaban kasar mu Nijeriya.

Ko akwai wasu ayyuka masu muhimmanci da za su saTalaka ya ji ya kamata ya sake zabar Tinubu?

Cikin manyan nasarorin da shugaban Tinubu ya samu a cikin shekarun da ya yi yana mulkin Nijeriya su ne yadda ya samar mana da tsaro a manyan hanyoyi da garuruwan kasar nan musamman a yankin arewacin Nijeriya. idan zan iya tunawa daya daga cikin dalilan da suka sa na ki zabar jam’iyyar APC a lokacin Marigayi Shugaba Buhari shi ne yadda matsalar tsaro ta ta’azzara, musamman kuma ganin yadda yawancin ‘yan arewa ne suke rike da mukaman da suka shafi bangaren tsaro. Tafiye-tafiye cikin kasa ya gagara saboda matsalar tsaro amma cikin ikon Allah tun daga hawan Shugaba Tinubu yanzu zaka iya tafiya daga Kaduna zuwa Abuja da wasu sassan kasar nan ba tare wani tsoro ko fargaba ba. Saboda a halin yanzu an samu sauki sosai. Lallai ya yi kokari sosai. A bangaren tattalin arzikiki kuma, lallai Shugaba Tinubu ya yi kokari sosasi, musamman a bangren abinci, farashin shinkafa da masara da sauransu sun yi tashin gwauron zabbi musamman a lokacin da aka janye tallafin man fetur amma cikin hikimar Tinubu a yanzu al’umma suna sayen abinci ba tare da takura ba. Wannan na daga cikin dalilan da zai sa ‘yan Nijeriya su rungumim tafiyar Tijnubu ba tare da wani matsala ba.

Wane irin gyara kake ganin ya kamata Tinubu ya yi kafin zaben 2027, wadanda za su karfafa samun nasararsa?

Gyaran da ta kamata Tijnubu ya yi a gabannin zaben 2027, ya riga ya yi su, kasancewar shi mutum ne mai son ci gaban kasa, tuni ya tabbatar da jihohi suna samun kudaden da ba a taba samun gwamnatin da ta ba jihohi ba. Ya kuma yi tsaye wajen ganin jihohin suna amfani da kudaden ne wajen gudanar da ayyukan raya kasa da bunkasa rayuwar talaka. Ya kuma tsayu wajen ganin ‘ya’yen talakawa sun samu ingantaccen ilimi a dukkan matakai musamman a manyan makarantun kasar nan, a kan haka ya kirkiro da tsarin ba ‘yan makarantun jami’a tallafin karatu da kudaden da za su sa a aljihu domin gudanar da karatunsu cikin natsuwa (NELFUND). Tabbas wadannna suna daga cikin manyan ayyukan da Tinubu ya yi da za su talaka ya zabe shi a 2027.

Zuwa yanzu an fara samun tayar da jijiyar wuya a wash jihohi sakamakon zaben fidda da gwamni na ‘yan takara, menene shawarar ka ga ‘yan siyasa?

Kira na ga ‘yan siyasa da suka fara tayar da jijiyan wuya sakamakon rashin nasara a zabukkan fidda ga gwani na jam’iyyar APC, musamman kamar irin su Farfesa Isa Pantami. Ya kamata su sani cewa, babu yadda za a yi a ba mutum biyu takarar gwamna a jiha daya, dole a samu wasu su yi hakuri, amma in har ka yi biyayya ka muna cewa kai mai kaunar nasarar jam’iyyar ce, kai ma kana iya samun wani babban rabo a nan gaba, amma in har ka nace da cewa dole sai  kai za a ba kuma ko da kai aka ba sai wasu sun yi gunagunii a kan haka ya kamata kowa ya kai zuciya nesa, ya zama kowa yana kokarin tabbatar da ganin jam’iyya ta yi nasara ne a dukkan matakai. A kan haka ina kira ga dukkan ‘yan jam’iyyarmu su kai zuciya nesa, su kuma bayar da goyon baya ga wanda aka zaba, ta haka za a samu nasarar da ya kamata.

Ko akwai wani jawabi da kake son yi wa ‘yan Nijeriya game da zaben 2027?

Jawabi na karshe ga ‘yan Nijeriya shi ne su kara hakuri tare da ba Shugaba Tinubu dukkan goyon bayan da ake bukata domin samun cikakkiyar nasara ga jam’iyyar APC a dukkan matakai na zabukkan da ke tafe. Tabbas za mu ga canji a harkokin gudanarwa kasar nan. Muna da yakinin Tinubu dan siyasa ne da ba a taba samun kamarsa ba a kasar, domin yana kishin ci gaban Nijeriya. Ya kuma shirya fito da tsare-tsaren da za su bukasda rayuwar al’umma a cikin kankanin lokaci. Allah ya ba mu sa a.

Mun gode sosai

Nima na gode

zangina
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Next Post
An Sake Karrama Gwamna Dauda Lawal Da Lambar Yabo Kan Mulki Na Adalci A Zamfara

An Sake Karrama Gwamna Dauda Lawal Da Lambar Yabo Kan Mulki Na Adalci A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.