ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Watsi Da Muslim-muslim Tiket Zai Iya Raunata APC — Ministar Al’adu

by Yusuf Shuaibu
5 months ago
Muslim

Ministar raya al’adu da yawon bude ido da tattalin arzikin kirkire-kirkire, Hannatu Musawa, ta yi gargadin cewa jam’iyyar APC za ta fuskanci barazanar a zaben 2027 idan ta yi watsi da Musulmin-muslim tiket a sake takarar Shugaban kasa Bola Tinubu.

Hannatu ta yi wannan gargadin ne a cikin wani tattauawa ta musamman da dan jarida Seun Okinbaloye, yayin da ake kara yawan jita-jitar cewa jam’iyyar mai mulki na iya la’akari da sauya tikitin Musulmi-Musulmi da aka yi amfani da shi a zaben shugaban kasa a 2023.

  • An Nada Liu Xianfa Wakilin Musamman Na Gwamnatin Sin Kan Harkokin Afirka
  • Fasahar Electronic Call-up Da NPA Ta Wanzar Ta Samar Da Sauki —Tsohon Kwaminsihan Sufuri

A cewar ministar, cire Kashim Shettima ko maye gurbinsa da abokin takara Musulmi wanda ba na Arewacin Nijeriya ba zai zama babban kalubale na siyasa ga APC, musamman a jihohin arewacin kasar.

ADVERTISEMENT

“Idan babu Musulmi Bahause ko Fulani ko Kanuri a wannan tikitin, hakan zai haifar da cikas. Wannan shi ne gaskiyar yadda mutane ke tunani,” in ji Hannatu.

Ta jaddada cewa siyasa a Arewacin Nijeriya ta tsayu sosai, tana gargadin cewa yanke shawara ba tare da cikakken fahimtar yankin ba na iya jefa kasa ciki matsala.

LABARAI MASU NASABA

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

“Asalin jihohin arewa kamar Katsina, Kano, Kaduna, Kebbi, Jigawa, Zamfara da Sakkwato, suna fahimtar siyasa a mataki mai zurfi sosai. A wannan yanki, siyasa hanya ce ta rayuwa. Mutane na jira duk bayan shekaru hudu don su tsaya a layi su kada kuri’a saboda a can suke jin suna da tasiri,” in ji ta.

Hannatu ta yi watsi da ikirarin cewa APC za ta iya samun narasa a zabe n shugabancin kasa cikin sauki ba tare da wani kalubale ba, tana bayyana irin wannan zato a matsayin rashin sanin siyasa.

“Ina tunani cewa idan muka yi wasa da sauya tsarin abin da muke da shi yanzu, hakan zai zama matsala. Mutanen da ke ba da shawara akasin haka watakila ba su fahimci yadda siyasa ke aiki a Arewa ba,” in ji ta.

Game da maganganu kan karuwar hadin gwiwar ‘yan adawa kafin 2027, Hannatu ta ce ba ta ganin tsarin jam’iyyun ‘yan adawa na yanzu zai iya kifar da Shugaba Tinubu da mataimakinsa Shettima ba.

Ta bayyana ‘yan adawar a matsayin wadanda suka samu rarrabun kawuna sakamakon rikicin shugabanci mai zafi a tsakaisu.

Yayin da ta amince cewa ‘yan adawa suna ci gaba da tafiya babu tasiri, ta tabbatar da cewa APC na da kwarin gwiwa na ci gaba da rike iko a kasar nan.

Hannatu ta kara da cewa ko da yake APC na maraba da jam’iyyun adawa don ci gaban dimokiradiyya, jam’iyyar mai mulki tana mai da hankali kan karfafa tushen siyasarta kafin zaben 2027.

Muslim
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

MASU ALAKA

makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

June 26, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Next Post
Tsare Okupe Ba Zai Hana Ni Zama Shugaban Kasa A 2023 Ba – Peter Obi 

ADC Ta Gargadi Magoya Bayan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar Gabanin Zaben Fitar Da Gwani

LABARAI MASU NASABA

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.