ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Watsi Da Muslim-muslim Tiket Zai Iya Raunata APC — Ministar Al’adu

by Yusuf Shuaibu
5 months ago
Muslim

Ministar raya al’adu da yawon bude ido da tattalin arzikin kirkire-kirkire, Hannatu Musawa, ta yi gargadin cewa jam’iyyar APC za ta fuskanci barazanar a zaben 2027 idan ta yi watsi da Musulmin-muslim tiket a sake takarar Shugaban kasa Bola Tinubu.

Hannatu ta yi wannan gargadin ne a cikin wani tattauawa ta musamman da dan jarida Seun Okinbaloye, yayin da ake kara yawan jita-jitar cewa jam’iyyar mai mulki na iya la’akari da sauya tikitin Musulmi-Musulmi da aka yi amfani da shi a zaben shugaban kasa a 2023.

  • An Nada Liu Xianfa Wakilin Musamman Na Gwamnatin Sin Kan Harkokin Afirka
  • Fasahar Electronic Call-up Da NPA Ta Wanzar Ta Samar Da Sauki —Tsohon Kwaminsihan Sufuri

A cewar ministar, cire Kashim Shettima ko maye gurbinsa da abokin takara Musulmi wanda ba na Arewacin Nijeriya ba zai zama babban kalubale na siyasa ga APC, musamman a jihohin arewacin kasar.

ADVERTISEMENT

“Idan babu Musulmi Bahause ko Fulani ko Kanuri a wannan tikitin, hakan zai haifar da cikas. Wannan shi ne gaskiyar yadda mutane ke tunani,” in ji Hannatu.

Ta jaddada cewa siyasa a Arewacin Nijeriya ta tsayu sosai, tana gargadin cewa yanke shawara ba tare da cikakken fahimtar yankin ba na iya jefa kasa ciki matsala.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

“Asalin jihohin arewa kamar Katsina, Kano, Kaduna, Kebbi, Jigawa, Zamfara da Sakkwato, suna fahimtar siyasa a mataki mai zurfi sosai. A wannan yanki, siyasa hanya ce ta rayuwa. Mutane na jira duk bayan shekaru hudu don su tsaya a layi su kada kuri’a saboda a can suke jin suna da tasiri,” in ji ta.

Hannatu ta yi watsi da ikirarin cewa APC za ta iya samun narasa a zabe n shugabancin kasa cikin sauki ba tare da wani kalubale ba, tana bayyana irin wannan zato a matsayin rashin sanin siyasa.

“Ina tunani cewa idan muka yi wasa da sauya tsarin abin da muke da shi yanzu, hakan zai zama matsala. Mutanen da ke ba da shawara akasin haka watakila ba su fahimci yadda siyasa ke aiki a Arewa ba,” in ji ta.

Game da maganganu kan karuwar hadin gwiwar ‘yan adawa kafin 2027, Hannatu ta ce ba ta ganin tsarin jam’iyyun ‘yan adawa na yanzu zai iya kifar da Shugaba Tinubu da mataimakinsa Shettima ba.

Ta bayyana ‘yan adawar a matsayin wadanda suka samu rarrabun kawuna sakamakon rikicin shugabanci mai zafi a tsakaisu.

Yayin da ta amince cewa ‘yan adawa suna ci gaba da tafiya babu tasiri, ta tabbatar da cewa APC na da kwarin gwiwa na ci gaba da rike iko a kasar nan.

Hannatu ta kara da cewa ko da yake APC na maraba da jam’iyyun adawa don ci gaban dimokiradiyya, jam’iyyar mai mulki tana mai da hankali kan karfafa tushen siyasarta kafin zaben 2027.

Muslim
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

MASU ALAKA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
Next Post
Tsare Okupe Ba Zai Hana Ni Zama Shugaban Kasa A 2023 Ba – Peter Obi 

ADC Ta Gargadi Magoya Bayan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar Gabanin Zaben Fitar Da Gwani

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026
Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

June 14, 2026
An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

June 14, 2026
Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

June 14, 2026
Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin

Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.