ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Watsi Da Muslim-muslim Tiket Zai Iya Raunata APC — Ministar Al’adu

by Yusuf Shuaibu
7 months ago
Muslim

Ministar raya al’adu da yawon bude ido da tattalin arzikin kirkire-kirkire, Hannatu Musawa, ta yi gargadin cewa jam’iyyar APC za ta fuskanci barazanar a zaben 2027 idan ta yi watsi da Musulmin-muslim tiket a sake takarar Shugaban kasa Bola Tinubu.

Hannatu ta yi wannan gargadin ne a cikin wani tattauawa ta musamman da dan jarida Seun Okinbaloye, yayin da ake kara yawan jita-jitar cewa jam’iyyar mai mulki na iya la’akari da sauya tikitin Musulmi-Musulmi da aka yi amfani da shi a zaben shugaban kasa a 2023.

  • An Nada Liu Xianfa Wakilin Musamman Na Gwamnatin Sin Kan Harkokin Afirka
  • Fasahar Electronic Call-up Da NPA Ta Wanzar Ta Samar Da Sauki —Tsohon Kwaminsihan Sufuri

A cewar ministar, cire Kashim Shettima ko maye gurbinsa da abokin takara Musulmi wanda ba na Arewacin Nijeriya ba zai zama babban kalubale na siyasa ga APC, musamman a jihohin arewacin kasar.

ADVERTISEMENT

“Idan babu Musulmi Bahause ko Fulani ko Kanuri a wannan tikitin, hakan zai haifar da cikas. Wannan shi ne gaskiyar yadda mutane ke tunani,” in ji Hannatu.

Ta jaddada cewa siyasa a Arewacin Nijeriya ta tsayu sosai, tana gargadin cewa yanke shawara ba tare da cikakken fahimtar yankin ba na iya jefa kasa ciki matsala.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

“Asalin jihohin arewa kamar Katsina, Kano, Kaduna, Kebbi, Jigawa, Zamfara da Sakkwato, suna fahimtar siyasa a mataki mai zurfi sosai. A wannan yanki, siyasa hanya ce ta rayuwa. Mutane na jira duk bayan shekaru hudu don su tsaya a layi su kada kuri’a saboda a can suke jin suna da tasiri,” in ji ta.

Hannatu ta yi watsi da ikirarin cewa APC za ta iya samun narasa a zabe n shugabancin kasa cikin sauki ba tare da wani kalubale ba, tana bayyana irin wannan zato a matsayin rashin sanin siyasa.

“Ina tunani cewa idan muka yi wasa da sauya tsarin abin da muke da shi yanzu, hakan zai zama matsala. Mutanen da ke ba da shawara akasin haka watakila ba su fahimci yadda siyasa ke aiki a Arewa ba,” in ji ta.

Game da maganganu kan karuwar hadin gwiwar ‘yan adawa kafin 2027, Hannatu ta ce ba ta ganin tsarin jam’iyyun ‘yan adawa na yanzu zai iya kifar da Shugaba Tinubu da mataimakinsa Shettima ba.

Ta bayyana ‘yan adawar a matsayin wadanda suka samu rarrabun kawuna sakamakon rikicin shugabanci mai zafi a tsakaisu.

Yayin da ta amince cewa ‘yan adawa suna ci gaba da tafiya babu tasiri, ta tabbatar da cewa APC na da kwarin gwiwa na ci gaba da rike iko a kasar nan.

Hannatu ta kara da cewa ko da yake APC na maraba da jam’iyyun adawa don ci gaban dimokiradiyya, jam’iyyar mai mulki tana mai da hankali kan karfafa tushen siyasarta kafin zaben 2027.

Muslim
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Tsare Okupe Ba Zai Hana Ni Zama Shugaban Kasa A 2023 Ba – Peter Obi 

ADC Ta Gargadi Magoya Bayan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar Gabanin Zaben Fitar Da Gwani

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.