ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ADC Ta Gargadi Magoya Bayan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar Gabanin Zaben Fitar Da Gwani

by Yusuf Shuaibu
4 months ago
ADC

An yi kiran ga goyon bayan duk ‘yan takarar shugaban kasa a jam’iyyar hadaka ta ADC da su daina yawan furta maganan da za su iya jawo rarrauwar kai, musamman ma magoya bayan Mista Peter Obi a gaban zabukan fad da gwai da za a yi a watan Yuni, 2026.

Jam’iyyar adawa ta yi wannan gargadin ne ta hanyar wani shirin tattaunawa na sauti kai tsaye da ya shafi halin da kasar ke ciki.

  • An Nada Liu Xianfa Wakilin Musamman Na Gwamnatin Sin Kan Harkokin Afirka
  • CGI Babandede Mai Ritaya A Mizanin Kyawawan Halaye Da Kwazon Aiki

Jam’iyyar ta kuma lura cewa gudanar da zaben 2027 a shekarar 2026 kamar yadda ake shawar yi zai zama tamkar takobi mai kaifi biyu gare ta, inda ta jaddada cewa jam’iyyar za ta sha wahala wajen yin shirin zaben.

ADVERTISEMENT

Duk da haka, ta nuna cewa gudanar da zaben kafin lokaci zai yi aiki ne ga jam’iyya a daya bangaren.

Sakataren yada labarai na kasa na ADC, Malam Bolaji Abdullahi, ya bayyana cewa ya yi wasu tattaunawa da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da tsohon dan takarar jam’iyyar LP a zaben 2023, Mista Peter Obi da tsohon Gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi da kuma wasu kamar tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai kan bukatar karfafa hadin kai da mayar da hankali da kuma jajircewar da za ta tabbatar da nasara a zaben da ke tafe.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Abdulllahi ya ce, “Na dauki tsawon lokaci ina magana da Atiku Abubakar, Peter Obi, Rotimi Amaechi wadanda suka nuna sha’awar yin takarar shugaban kasa a jam’iyyarmu, haka kuma na tattauna da irin su Malam Nasir El-Rufai don karfafa jam’iyyarmu da hadin kai don seta alkiblar wannan kasa ta zama wuri mafi kyau.

“Dukkan shugabanninmu sun sani game da aikin da ke gabanmu, kuma kowannensu ya himmatu wajen tabbatar da cewa mun ci wannan zaben.”

Bugu da kari a kan haka, ya ce ko za a gudanar da zabe a wannan shekara ko shekara mai zuwa zai kasance aiki biyu ga jam’iyyar.

Sakataren jam’iyyar ya kuma ce suna daukar zaben kananan hukumomin Abuja da matukar muhimmanci, yana nuna cewa sun kasa samun nasara a zaben cike guri a Jihar Anambra, don haka, suke wannan bayanin.

Haka kuma ya bayyana damuwarsa kan yadda gwamnatin Jihar Legas ke kwatanta ma’aikatan gwamnati da lambar shaida ta kasa don yin rajista a matsayin mambobin APC.

A wani labarin mai kama da wannan, ADC ta rubuta wa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) wasikar na neman daga zaben  kanana hukumomin Babban Birnin Tarayya Abuja da aka shirya a ranar Asabar, 21 ga Fabrairu, 2026, saboda azumin watab Ramadan.

A cikin wasikar da aka rubuta a ranar 22 ga Janairu, 2026, wacce ta samu sa hannun shugaban jam’iyyar, Sanata Dabid A. B. Mark, da sakataren jam’iyyar, Ogbeni Rauf Aregbesola, jam’iyyar ta jawo hankalin hukumar zabe kan cewa, ranar zaben da aka tsara ana cikin lokacin azumin Ramadan, wanda mafi yawan masu zabe na iya kaurace masa.

ADC ta rabuta a cikin wasikar cewa, dangane daukar muhimmancin al’adu da addini a wannan lokaci ya zama dole a sake duba ranar zabe. Don haka, jam’iyyar ta roki INEC cikin girmamawa ta jinkirta zaben zuwa bayan watan Ramadan.

Wasikar ta kara jaddada cewa bukatar ta samo asali ne daga bukatar kare hadin kai a tsarin zabe, inda ta bayyana cewa an yi ta ne domin cimma tsarin zabe mai tsari wanda ke ba dukkan ‘yan kasa ‘yancisu ba tare da la’akari da addini ba da damar amfani da cikakkiyar hakkokinsu na ‘yan ba tare da wani kuntatawa ko rashin fa’ida ba.

ADC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Ƴansanda Sun Kama Mutane Uku Kan Siyan Motar Miliyan 75 Amma Suka Tura Kuɗin Bogi

Ƴansanda Sun Kama Mutane Uku Kan Siyan Motar Miliyan 75 Amma Suka Tura Kuɗin Bogi

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.