ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ADC Ta Gargadi Magoya Bayan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar Gabanin Zaben Fitar Da Gwani

by Yusuf Shuaibu
7 months ago
ADC

An yi kiran ga goyon bayan duk ‘yan takarar shugaban kasa a jam’iyyar hadaka ta ADC da su daina yawan furta maganan da za su iya jawo rarrauwar kai, musamman ma magoya bayan Mista Peter Obi a gaban zabukan fad da gwai da za a yi a watan Yuni, 2026.

Jam’iyyar adawa ta yi wannan gargadin ne ta hanyar wani shirin tattaunawa na sauti kai tsaye da ya shafi halin da kasar ke ciki.

  • An Nada Liu Xianfa Wakilin Musamman Na Gwamnatin Sin Kan Harkokin Afirka
  • CGI Babandede Mai Ritaya A Mizanin Kyawawan Halaye Da Kwazon Aiki

Jam’iyyar ta kuma lura cewa gudanar da zaben 2027 a shekarar 2026 kamar yadda ake shawar yi zai zama tamkar takobi mai kaifi biyu gare ta, inda ta jaddada cewa jam’iyyar za ta sha wahala wajen yin shirin zaben.

ADVERTISEMENT

Duk da haka, ta nuna cewa gudanar da zaben kafin lokaci zai yi aiki ne ga jam’iyya a daya bangaren.

Sakataren yada labarai na kasa na ADC, Malam Bolaji Abdullahi, ya bayyana cewa ya yi wasu tattaunawa da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da tsohon dan takarar jam’iyyar LP a zaben 2023, Mista Peter Obi da tsohon Gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi da kuma wasu kamar tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai kan bukatar karfafa hadin kai da mayar da hankali da kuma jajircewar da za ta tabbatar da nasara a zaben da ke tafe.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

Abdulllahi ya ce, “Na dauki tsawon lokaci ina magana da Atiku Abubakar, Peter Obi, Rotimi Amaechi wadanda suka nuna sha’awar yin takarar shugaban kasa a jam’iyyarmu, haka kuma na tattauna da irin su Malam Nasir El-Rufai don karfafa jam’iyyarmu da hadin kai don seta alkiblar wannan kasa ta zama wuri mafi kyau.

“Dukkan shugabanninmu sun sani game da aikin da ke gabanmu, kuma kowannensu ya himmatu wajen tabbatar da cewa mun ci wannan zaben.”

Bugu da kari a kan haka, ya ce ko za a gudanar da zabe a wannan shekara ko shekara mai zuwa zai kasance aiki biyu ga jam’iyyar.

Sakataren jam’iyyar ya kuma ce suna daukar zaben kananan hukumomin Abuja da matukar muhimmanci, yana nuna cewa sun kasa samun nasara a zaben cike guri a Jihar Anambra, don haka, suke wannan bayanin.

Haka kuma ya bayyana damuwarsa kan yadda gwamnatin Jihar Legas ke kwatanta ma’aikatan gwamnati da lambar shaida ta kasa don yin rajista a matsayin mambobin APC.

A wani labarin mai kama da wannan, ADC ta rubuta wa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) wasikar na neman daga zaben  kanana hukumomin Babban Birnin Tarayya Abuja da aka shirya a ranar Asabar, 21 ga Fabrairu, 2026, saboda azumin watab Ramadan.

A cikin wasikar da aka rubuta a ranar 22 ga Janairu, 2026, wacce ta samu sa hannun shugaban jam’iyyar, Sanata Dabid A. B. Mark, da sakataren jam’iyyar, Ogbeni Rauf Aregbesola, jam’iyyar ta jawo hankalin hukumar zabe kan cewa, ranar zaben da aka tsara ana cikin lokacin azumin Ramadan, wanda mafi yawan masu zabe na iya kaurace masa.

ADC ta rabuta a cikin wasikar cewa, dangane daukar muhimmancin al’adu da addini a wannan lokaci ya zama dole a sake duba ranar zabe. Don haka, jam’iyyar ta roki INEC cikin girmamawa ta jinkirta zaben zuwa bayan watan Ramadan.

Wasikar ta kara jaddada cewa bukatar ta samo asali ne daga bukatar kare hadin kai a tsarin zabe, inda ta bayyana cewa an yi ta ne domin cimma tsarin zabe mai tsari wanda ke ba dukkan ‘yan kasa ‘yancisu ba tare da la’akari da addini ba da damar amfani da cikakkiyar hakkokinsu na ‘yan ba tare da wani kuntatawa ko rashin fa’ida ba.

ADC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Ƴansanda Sun Kama Mutane Uku Kan Siyan Motar Miliyan 75 Amma Suka Tura Kuɗin Bogi

Ƴansanda Sun Kama Mutane Uku Kan Siyan Motar Miliyan 75 Amma Suka Tura Kuɗin Bogi

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.