ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

by Yusuf Shuaibu
2 weeks ago
Zaben

‘Yan takarar shugaban kasa a 2027 sun bude wani sabon babi bayan an bude yakin neman zabe a hukumance a ranar Laraba da ta gabata.

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da tsohon gwamnan Jihar Anambra, Peter Obi, sun zabi hanyoyi daban-daban don tallata kansu a ranar farko ta yakin neman zaben 2027.

Yayin da Tinubu ya zabi ganawa da ‘yan siyasa da masu ruwa da tsaki na ranar farko na yakin neman zabensa karo na biyu, Atiku ya tafi kai tsaye ga ‘yan Nijeriya ta hanyar yin bidiyo kai tsayi a shafinsa na sada zumunta na Facebook, yana amfani da dandalin wajen suka ga manufofin tattalin arziki na gwamnatin Tinubu.

ADVERTISEMENT

A gefe guda kuma, Obi ya kaddamar da yakin neman zabensa da sakon da ya ta’allaka kan kwarewarsa da halinsa da jawo hankalin bukatar masu jefa kuri’a da kuma duba manufofin wadanda ke neman mulkar kasar.

Hanyoyin da ‘yan takarar shugaban kasa suka dauka na yakin neman zabe sun bambanta, yayin da aka kada gaggan yakin neman zaben shugaban kasa a hukumance a ranar 19 ga Agusta, 2026, kafin zaben shugaban kasa na ranar 16 ga Janairu, 2027.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

Haka kuma ‘yan takarar shugaban kasa sun rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a Abuja, sun yi alkawarin gudanar da yakin neman zaben cikin lumana da maida hankali kan batutuwa masu amfanar da al’ummar Nijeriya.

Tinubu a ranar farko bai fara da taron kamfen na shugaban kasa kamar yadda aka saba ba na kaddamar da yakin neman zabe mai daukar hankali ba.

Maimakon haka, ya zauna a fadar shugaban kasa da ke Abuja ya jagoranci taron kwamitin zartarwa na tarayya, taronsa na farko tun bayan ranar 29 ga Yuni, 2026.

Yayin da takwarorinsa suka fara bayyana hujjojinsu ga masu jefa kuri’a, Tinubu ya ci gaba da nuna ayyukan da ya gudanr a shugabancinsa da ke mai da hankali kan gwamnati.

Taron kwamitin zartarwar ya dauki wasu matakai game da tattalin arziki da ilimi da ababen more rayuwa da sauran fannonin gudanarwa.

Shi kuwa, Atiku a ranar farko ta yakin neman zabe ta ba shi damar kai tsaye kan tattauna batun tattalin arzikin kasar nan.

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar ADC ya yi amfani da shafinsa na Facebook a ranar Laraba wajen alkawarin cewa zai mayar da tallafin man fetur idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa a 2027.

Atiku ya kalubalanci matakin da gwamnatin Tinubu ta dauka na cire tallafin mai.

Ya tambayi abin da ake yi da kudin da aka samu bayan dakatar da tallafin, yana jayayya cewa ya kamata ‘yan Nijeriya su ga fa’idodi a bayyane daga wannan tsarin ta hanyar gudanar da ingantattun ayyukan raya kasa.

Sakon nasa ya sanya ayoyin tambaya kan cire tallafi a jawabin farko na yakin neman zabe, yana bai wa masu zabe wani sabon shiri da ya bambanta da manufar Tinubu.

Atiku ya kuma yi amfani da fara kamfen din don neman karin bayani kan kudaden da gwamnati ke kashewa.

Amma shi kuwa Obi a ranar farko bai yi bayani kan sauyin manufofi mai daukar hankali ba, sai dai ya yi ne game da kafa sharuddan da yake so ‘yan Nijeriya su yi amfani da su wajen hukunci kan zaben shugaban kasa.

Ofishin yada labaransa ya gabatar da shi a matsayin dan takarar da ke da hankali, yana kira ga ‘yan Nijeriya da su yi amfani da kwanaki 150 na kamfen don duba tarihi, halaye da shawarwarin manufofin dukkan ‘yan takarar shugaban kasa.

Sakon bude kamfen na dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NDC ya fi mai da hankali ne kan zaban cancanta maimakon yin alkawari kan wasu shirye-shirye.

Tawagar yakin neman zabensa ta yi hujjar cewa yakin neman zaben ya kamata ya zama dama ga ‘yan Nijeriya su binciki karfin wadanda ke neman shugabancin kasa kuma su duba tarihinsu na baya kan alkawuran da suke yi wa masu jefa kuri’a.

Shirin da Obi ya gabatar ya hada da ci gaban Nijeriya daga cima zaune zuwa masu fitarwa ta hanyar masana’antu, rage yawan kudin gudanarwa, karfafa ilimi da kiwon lafiya, inganta tsaro da samar da karin damar tattalin arziki.

Wannan sakon yana da daidaito da matsayin siyasa da Obi yake kokarin ginawa game da habakar tattalin arziki.

Hanyoyi uku sun ba da hasashen farko na yadda yakin neman zabe zai iya faruwa a cikin watannin masu zuwa.

Tinubu, a matsayin wanda ke rike da mukamin yanzu, ya farawa daga matsayin samun damar yin yakin neman zabe bisa tarihin mulkin da yake yi, wanda ya dauki manyan matakan tattalin arziki, yayin da kuma yake kare wadannan matakan da tasirinsu ga rayuwar ‘yan Nijeriya.

Atiku na neman juyar da rashin jin dadin mutane zuwa hujja don sauyi na siyasa, inda ya yi alkawarin dawo da tallafin man fetur ya zama daya daga cikin alkawuran da ya fara dauka idan aka zabe shi.

A nasa bangaren, Obi na kokarin sanya kwarewa, daukar alhakin da inganta tattalin arziki su kasance tambayoyi da za su yi tasiri a zaben.

Saboda haka, ya roki masu zabe su kimanta ‘yan takara fiye da tsarin jam’iyya, taron yakin neman zabe da kuma taken siyasa.

Ranar farko na bude yakin nema zaben ta bayyana fiye da ayyukan kowane daya daga cikin manyan ‘yan takara guda uku.

Ta bayar da alamar farko na hujjojin da kowane dan takara yake shirin gabatarwa ga masu jefa kuri’a.

Sakonnin farko na manyan ‘yan takara guda uku za a iya juya su zuwa goyon bayan masu jefa kuri’a a yayin da kamfen din 2027 ke samun karfi.

Zaben
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Ƴan Nijeriya Za Su Kori APC Idan Har An Gudanar Da Sahihin Zaɓe – Shugaban PRP

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Xi Ya Jagoranci Taron Shugabanni Na JKS Kan Ayyukan Ceto Bayan Zabtarewar Kasa A Gundumar Gyirong

Xi Ya Jagoranci Taron Shugabanni Na JKS Kan Ayyukan Ceto Bayan Zabtarewar Kasa A Gundumar Gyirong

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.