ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Ƴan Nijeriya Za Su Kori APC Idan Har An Gudanar Da Sahihin Zaɓe – Shugaban PRP

by Yusuf Shuaibu
3 weeks ago
Nijeriya

Shugaban jam’iyyar PRP na ƙasa, Dakta Hakeem Baba-Ahmed, ya bayyana cewa ƴan Nijeriya za su kori jam’iyyar APC mai mulki a shekarar 2027, muddin idan aka gudanar da sahihin zaɓe yam ai cike da adalci.

Baba-Ahmed ya yi iƙirarin cewa babban abin da ya kamata APC ta damu da shi ba jam’iyyun siyasa na adawa ba, amma ta damu da ƴan Nijeriya masu kaɗa kuri’a, waɗanda su ne za su yanke hukunci na ƙasarshe a zaɓen 2027.

Ya yi waɗannan sharhi ne yayin da yake tattaunawa kan sake tsara haɗin gwiwar siyasa da dabarun adawa kafin zaɓukan shekarar 2027 a wani shiri na gidan talabijin Alheri a Jihar Kaduna.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, jam’iyyun siyasa ba su yanke sakamakon zaɓe, masu jefa ƙuri’a su ne ke yanke wane ƴan takara da jam’iyyun za su yi nasara.

“Suna sane cewa idan suka bari aka gudanar da sahihin zaɓe mai cike da gaskiya, ƴan Nijeriya ba za su kaɗa ƙuri’a a gare su ba. Wannan shi ne abin da suke tsoron,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

Shugaban PRP ya ƙara da cewa, “Ba saboda hamayya daga wasu jam’iyyun siyasa suke kamata su ji tsoro ba, sai dai hamayya daga ƴan Nijeriya, domin jam’iyyun siyasa ba sa kaɗa ƙuri’a, ƴan Nijeriya ne suke kaɗa ƙuri’a.”

Ya ce APC ta san cewa bari ƴan ƙasa su zaɓi shugabanninsu cikin ƴanci zai iya zama abin da zai sa jam’iyyar ta yi rashin nasara a 2027.

Baba-Ahmed ya kuma gargaɗi ƴan adawa game da sake ƙirƙiro haɗin kai don fatattakar Shugaba Bola Ahmed Tinubu ba tare da samun shiri mai kyau da ba.

“Mun sani akwai wasu mutane da kawai suke neman a cire Tinubu domin su yi abin da suke so, ko su maimaita irin manufofin da Tinubu yake aiwatarwa a yanzu. Daga baya, watakila su ce an samu kuskure,” ya yi gargaɗi.

Ya jaddada cewa PRP ba zai goyi bayan wani ɗan siyasa ba kawai bisa ga burinsa na zama shugaban ƙasa.

“A PRP, ba za mu yarda mu goyi bayan wani kawai saboda yana da burin zama shugaban ƙasa ba. Ba za mu shiga irin wannan tsari ba. Dole mu fara ganin abin da suke niyya kafin mu yarda da su,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa kowace haɗin gwiwar siyasa da PRP ta goyi baya dole ne ta sami tsare-tsare bayyananne na magance manyan matsalolin Nijeriya, kamar rashin tsaro, talauci, yunwa, da rashin jin daɗin jama’a gaba ɗaya.

Baba-Ahmed ya lura cewa jam’iyyar za ta duba haɗin gwiwar siyasa da ke tasowa kafin shekarar 2027 domin tantance ko sun samo asali ne daga ainihin niyyoyi ko son zuciyar siyasa ta ƙashin kai.

“Za mu iya gane yaudara, kuma za mu iya gane kyakkyawan nufi,” in ji shi.

Ya ce a shirye jam’iyyarsa take domin yin haɗakar da zai kayar da Tinubu a zaɓen 2027, idan ƴan adawa sun haɗa kai a tsakaninsu kafin zaɓen.

Nijeriya
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Nijeriya
Siyasa

Muna Da Yan Takarar Gwamna A Jihohi 28 Don Shiga Zaben 2027

September 6, 2026
Next Post
Nijeriya

Shekaru 8 Cikin Raɗaɗi: Wani Bawan Allah Ya Samu Tiyata Kyauta Daga Gidauniyar Mangal

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.