ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027:Kwamishinoni 6 Sun Yi Murabus A Jihar Bauchi

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
1 month ago
Bala Mohammed

Babban Sakataren Gwamnatin Jihar Bauchi, Hon. Aminu Hassan Gamawa, tare da kwamishinoni shida sun yi murabus daga Majalisar Zartarwa ta Jihar (SEC) domin neman cikar burin siyasa gabanin zaben 2027.

Wadanda suka yi murabus sun hada da Yakubu Adamu (Ma’aikatar Kudi da Ci gaban Tattalin Arziki), Abdurrazak Nuhu Zaki (Ma’aikatar Albarkatun Ruwa), Hajara Yakubu Wanka (Ma’aikatar Harkokin Jin Kai da Agajin Gaggawa), Isa Babayo Tilde (Ma’aikatar Kananan Hukumomi da Harkokin Masarautu), Hon. Faruk Mustapha (Ma’aikatar Ci gaban Karkara da Ayyuka na Musamman), da sauransu.

Bayan murabus din, Gwamna Bala Mohammed ya amince da sauye-sauye cikin gaggawa tare da bai wa wasu mambobin majalisar zartarwa alhakin kula da ma’aikatun da abin ya shafa har sai an nada sabbin kwamishinoni.

ADVERTISEMENT

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Mukhtar Gidado, ya fitar jiya, an umarci Hashimu Yakubu, Babban Sakataren Sirri na Musamman (PPS), da ya kula da ofishin Babban Sakataren Gwamnati.

Gwamnan ya kuma tura tsohon kwamishinan ilimi, Dakta Mohammed Lawal Rimin Zayam, a matsayin kwamishina na Ma’aikatar Wutar Lantarki, Kimiyya da Fasaha.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Haka kuma, Babban Lauyan Jiha kuma Kwamishinan Shari’a, Hassan Usman El-Yakub (SAN), zai kula da Ma’aikatar Kananan Hukumomi da Harkokin Masarautu, yayin da Kwamishinan Yada Labarai da Sadarwa, Usman Usman Shehu, zai jagoranci kula da Ma’aikatar Albarkatun Ruwa.

Hakazalika, Kwamishinan Gidaje da Muhalli, Hon. Danlami Ahmed Kawule, an ba shi alhakin kula da Ma’aikatar Ci gaban Karkara da Ayyuka na Musamman, yayin da Amina Muhammad Katagum, Kwamishinar Kasafin Kudi, Tsare-tsare da Hadin Gwiwa na Kasashe, za ta kula da Ma’aikatar Harkokin Jin Kai da Agajin Gaggawa.

Bugu da kari, Mohammed Sadik Shira, Kwamishinan Harkokin Kungiyoyi da Kanana da Matsakaitan Masana’antu (SMEs), zai kula da Ma’aikatar Kudi da Ci gaban Tattalin Arziki, yayin da tsohon Mataimakin Sufeto Janar na ‘Yansanda (DIG mai ritaya) Sani Mohammed, mai ba gwamna shawara kan harkokin tsaro, zai kula da Ma’aikatar Tsaron Cikin Gida da Harkokin Jama’a.

Yayin da yake yi wa wadanda suka yi murabus fatan alheri a sabbin matakan da za su shiga, Gwamna Bala Mohammed ya bukaci wadanda aka sake tura su da su dauki cikakken alhakin ayyukansu tare da amfani da kwarewarsu wajen tafiyar da ma’aikatun.

Ya kuma umarce su da su yi aiki tare da manyan sakatarorin ma’aikatun domin tabbatar da ci gaba da gudanar da ayyukan gwamnati ba tare da tangarda ba.

Bauchi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
Bauchi
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada

An Yi Kira Da A Kara Tallafi Kan Lamarin Yaran Da Ba Su Zuwa Makaranta

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.