ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027:Kwamishinoni 6 Sun Yi Murabus A Jihar Bauchi

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
4 weeks ago
Bala Mohammed

Babban Sakataren Gwamnatin Jihar Bauchi, Hon. Aminu Hassan Gamawa, tare da kwamishinoni shida sun yi murabus daga Majalisar Zartarwa ta Jihar (SEC) domin neman cikar burin siyasa gabanin zaben 2027.

Wadanda suka yi murabus sun hada da Yakubu Adamu (Ma’aikatar Kudi da Ci gaban Tattalin Arziki), Abdurrazak Nuhu Zaki (Ma’aikatar Albarkatun Ruwa), Hajara Yakubu Wanka (Ma’aikatar Harkokin Jin Kai da Agajin Gaggawa), Isa Babayo Tilde (Ma’aikatar Kananan Hukumomi da Harkokin Masarautu), Hon. Faruk Mustapha (Ma’aikatar Ci gaban Karkara da Ayyuka na Musamman), da sauransu.

Bayan murabus din, Gwamna Bala Mohammed ya amince da sauye-sauye cikin gaggawa tare da bai wa wasu mambobin majalisar zartarwa alhakin kula da ma’aikatun da abin ya shafa har sai an nada sabbin kwamishinoni.

ADVERTISEMENT

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Mukhtar Gidado, ya fitar jiya, an umarci Hashimu Yakubu, Babban Sakataren Sirri na Musamman (PPS), da ya kula da ofishin Babban Sakataren Gwamnati.

Gwamnan ya kuma tura tsohon kwamishinan ilimi, Dakta Mohammed Lawal Rimin Zayam, a matsayin kwamishina na Ma’aikatar Wutar Lantarki, Kimiyya da Fasaha.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Haka kuma, Babban Lauyan Jiha kuma Kwamishinan Shari’a, Hassan Usman El-Yakub (SAN), zai kula da Ma’aikatar Kananan Hukumomi da Harkokin Masarautu, yayin da Kwamishinan Yada Labarai da Sadarwa, Usman Usman Shehu, zai jagoranci kula da Ma’aikatar Albarkatun Ruwa.

Hakazalika, Kwamishinan Gidaje da Muhalli, Hon. Danlami Ahmed Kawule, an ba shi alhakin kula da Ma’aikatar Ci gaban Karkara da Ayyuka na Musamman, yayin da Amina Muhammad Katagum, Kwamishinar Kasafin Kudi, Tsare-tsare da Hadin Gwiwa na Kasashe, za ta kula da Ma’aikatar Harkokin Jin Kai da Agajin Gaggawa.

Bugu da kari, Mohammed Sadik Shira, Kwamishinan Harkokin Kungiyoyi da Kanana da Matsakaitan Masana’antu (SMEs), zai kula da Ma’aikatar Kudi da Ci gaban Tattalin Arziki, yayin da tsohon Mataimakin Sufeto Janar na ‘Yansanda (DIG mai ritaya) Sani Mohammed, mai ba gwamna shawara kan harkokin tsaro, zai kula da Ma’aikatar Tsaron Cikin Gida da Harkokin Jama’a.

Yayin da yake yi wa wadanda suka yi murabus fatan alheri a sabbin matakan da za su shiga, Gwamna Bala Mohammed ya bukaci wadanda aka sake tura su da su dauki cikakken alhakin ayyukansu tare da amfani da kwarewarsu wajen tafiyar da ma’aikatun.

Ya kuma umarce su da su yi aiki tare da manyan sakatarorin ma’aikatun domin tabbatar da ci gaba da gudanar da ayyukan gwamnati ba tare da tangarda ba.

Bauchi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Bauchi
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada

An Yi Kira Da A Kara Tallafi Kan Lamarin Yaran Da Ba Su Zuwa Makaranta

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.