ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027:Kwamishinoni 6 Sun Yi Murabus A Jihar Bauchi

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
2 months ago
Bala Mohammed

Babban Sakataren Gwamnatin Jihar Bauchi, Hon. Aminu Hassan Gamawa, tare da kwamishinoni shida sun yi murabus daga Majalisar Zartarwa ta Jihar (SEC) domin neman cikar burin siyasa gabanin zaben 2027.

Wadanda suka yi murabus sun hada da Yakubu Adamu (Ma’aikatar Kudi da Ci gaban Tattalin Arziki), Abdurrazak Nuhu Zaki (Ma’aikatar Albarkatun Ruwa), Hajara Yakubu Wanka (Ma’aikatar Harkokin Jin Kai da Agajin Gaggawa), Isa Babayo Tilde (Ma’aikatar Kananan Hukumomi da Harkokin Masarautu), Hon. Faruk Mustapha (Ma’aikatar Ci gaban Karkara da Ayyuka na Musamman), da sauransu.

Bayan murabus din, Gwamna Bala Mohammed ya amince da sauye-sauye cikin gaggawa tare da bai wa wasu mambobin majalisar zartarwa alhakin kula da ma’aikatun da abin ya shafa har sai an nada sabbin kwamishinoni.

ADVERTISEMENT

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Mukhtar Gidado, ya fitar jiya, an umarci Hashimu Yakubu, Babban Sakataren Sirri na Musamman (PPS), da ya kula da ofishin Babban Sakataren Gwamnati.

Gwamnan ya kuma tura tsohon kwamishinan ilimi, Dakta Mohammed Lawal Rimin Zayam, a matsayin kwamishina na Ma’aikatar Wutar Lantarki, Kimiyya da Fasaha.

LABARAI MASU NASABA

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

Haka kuma, Babban Lauyan Jiha kuma Kwamishinan Shari’a, Hassan Usman El-Yakub (SAN), zai kula da Ma’aikatar Kananan Hukumomi da Harkokin Masarautu, yayin da Kwamishinan Yada Labarai da Sadarwa, Usman Usman Shehu, zai jagoranci kula da Ma’aikatar Albarkatun Ruwa.

Hakazalika, Kwamishinan Gidaje da Muhalli, Hon. Danlami Ahmed Kawule, an ba shi alhakin kula da Ma’aikatar Ci gaban Karkara da Ayyuka na Musamman, yayin da Amina Muhammad Katagum, Kwamishinar Kasafin Kudi, Tsare-tsare da Hadin Gwiwa na Kasashe, za ta kula da Ma’aikatar Harkokin Jin Kai da Agajin Gaggawa.

Bugu da kari, Mohammed Sadik Shira, Kwamishinan Harkokin Kungiyoyi da Kanana da Matsakaitan Masana’antu (SMEs), zai kula da Ma’aikatar Kudi da Ci gaban Tattalin Arziki, yayin da tsohon Mataimakin Sufeto Janar na ‘Yansanda (DIG mai ritaya) Sani Mohammed, mai ba gwamna shawara kan harkokin tsaro, zai kula da Ma’aikatar Tsaron Cikin Gida da Harkokin Jama’a.

Yayin da yake yi wa wadanda suka yi murabus fatan alheri a sabbin matakan da za su shiga, Gwamna Bala Mohammed ya bukaci wadanda aka sake tura su da su dauki cikakken alhakin ayyukansu tare da amfani da kwarewarsu wajen tafiyar da ma’aikatun.

Ya kuma umarce su da su yi aiki tare da manyan sakatarorin ma’aikatun domin tabbatar da ci gaba da gudanar da ayyukan gwamnati ba tare da tangarda ba.

Bauchi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Kaddamar Da Atisayen Hadin Gwiwa Mai Taken “Hadin Gwiwar Ayyuka Kan Teku-2026” Tsakanin Sin Da Rasha
  • Sulaiman
    Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin
  • Sulaiman
    An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”
  • Sulaiman
    Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa
Bauchi
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas

MASU ALAKA

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata
Manyan Labarai

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

July 6, 2026
Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi
Manyan Labarai

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

July 6, 2026
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

July 6, 2026
Next Post
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada

An Yi Kira Da A Kara Tallafi Kan Lamarin Yaran Da Ba Su Zuwa Makaranta

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Atisayen Hadin Gwiwa Mai Taken “Hadin Gwiwar Ayyuka Kan Teku-2026” Tsakanin Sin Da Rasha

An Kaddamar Da Atisayen Hadin Gwiwa Mai Taken “Hadin Gwiwar Ayyuka Kan Teku-2026” Tsakanin Sin Da Rasha

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

July 6, 2026
Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

July 6, 2026
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

July 6, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

July 6, 2026
Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

July 6, 2026
Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

July 6, 2026
FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.