Babban Sakataren Gwamnatin Jihar Bauchi, Hon. Aminu Hassan Gamawa, tare da kwamishinoni shida sun yi murabus daga Majalisar Zartarwa ta Jihar (SEC) domin neman cikar burin siyasa gabanin zaben 2027.
Wadanda suka yi murabus sun hada da Yakubu Adamu (Ma’aikatar Kudi da Ci gaban Tattalin Arziki), Abdurrazak Nuhu Zaki (Ma’aikatar Albarkatun Ruwa), Hajara Yakubu Wanka (Ma’aikatar Harkokin Jin Kai da Agajin Gaggawa), Isa Babayo Tilde (Ma’aikatar Kananan Hukumomi da Harkokin Masarautu), Hon. Faruk Mustapha (Ma’aikatar Ci gaban Karkara da Ayyuka na Musamman), da sauransu.
Bayan murabus din, Gwamna Bala Mohammed ya amince da sauye-sauye cikin gaggawa tare da bai wa wasu mambobin majalisar zartarwa alhakin kula da ma’aikatun da abin ya shafa har sai an nada sabbin kwamishinoni.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Mukhtar Gidado, ya fitar jiya, an umarci Hashimu Yakubu, Babban Sakataren Sirri na Musamman (PPS), da ya kula da ofishin Babban Sakataren Gwamnati.
Gwamnan ya kuma tura tsohon kwamishinan ilimi, Dakta Mohammed Lawal Rimin Zayam, a matsayin kwamishina na Ma’aikatar Wutar Lantarki, Kimiyya da Fasaha.
Haka kuma, Babban Lauyan Jiha kuma Kwamishinan Shari’a, Hassan Usman El-Yakub (SAN), zai kula da Ma’aikatar Kananan Hukumomi da Harkokin Masarautu, yayin da Kwamishinan Yada Labarai da Sadarwa, Usman Usman Shehu, zai jagoranci kula da Ma’aikatar Albarkatun Ruwa.
Hakazalika, Kwamishinan Gidaje da Muhalli, Hon. Danlami Ahmed Kawule, an ba shi alhakin kula da Ma’aikatar Ci gaban Karkara da Ayyuka na Musamman, yayin da Amina Muhammad Katagum, Kwamishinar Kasafin Kudi, Tsare-tsare da Hadin Gwiwa na Kasashe, za ta kula da Ma’aikatar Harkokin Jin Kai da Agajin Gaggawa.
Bugu da kari, Mohammed Sadik Shira, Kwamishinan Harkokin Kungiyoyi da Kanana da Matsakaitan Masana’antu (SMEs), zai kula da Ma’aikatar Kudi da Ci gaban Tattalin Arziki, yayin da tsohon Mataimakin Sufeto Janar na ‘Yansanda (DIG mai ritaya) Sani Mohammed, mai ba gwamna shawara kan harkokin tsaro, zai kula da Ma’aikatar Tsaron Cikin Gida da Harkokin Jama’a.
Yayin da yake yi wa wadanda suka yi murabus fatan alheri a sabbin matakan da za su shiga, Gwamna Bala Mohammed ya bukaci wadanda aka sake tura su da su dauki cikakken alhakin ayyukansu tare da amfani da kwarewarsu wajen tafiyar da ma’aikatun.
Ya kuma umarce su da su yi aiki tare da manyan sakatarorin ma’aikatun domin tabbatar da ci gaba da gudanar da ayyukan gwamnati ba tare da tangarda ba.















Discussion about this post