Masana harkar ilimi sun yi kira da karin samun ci gaban harkar ilimi don haka ne ma suka ankarar da gwamnatocin
Kano, Katsina da kuma Jigawa da su ware ma bangaren ilimi wani kaso mai gwabi saboda kulawar yaro, da ci gaban ilimi, a matsayin wani mataki ne da ya zama dole ne a dauke shi da muhimmanci don a samu dama wajen daukar shi ya kuma dace da yaran da basu zuwa makarantai.
An yi wannan kiran ne lokacin da aka yi taron kwana biyu da ya shafi ganawa da manema labarai domin bunkasa bunkasa ilimin farko da yaro / yara za su fa samu, da kuma fadada hanyar da za a samu ilimi mai nagarta a Jihohin ukun,da aka yi a Dutse, hedikwatar Jihar Jigawa.Gidauniyar kasa da kasa da take kulawa da lamurran da suka shafi kananan yara tare da tallafi tarayyar Turai.
Da ake gabatar da wani jawabin wasika mai taken da ake kira “Zuba jari a farkon rayuwar ilimin rayuwar farko ta yara a matsayin wani ginshiki ne na rage yaran da ba su zuwa makaranata,” wanda masani ne akan rayuwar fako ta yaro, Dakta.Sunday Jacob, ya bayyana Kano, Katsina da kuma Jigawa suka samar da kashi kusan 30 na yaran da basu zuwa makaranta a Nijeriya, lamarin da aka alakanta shi da fatara, tabarbarewar tsaro, koma babu shi tsaron, da kuma yadda al’ada take taka rawa, ga kuma nisan tafiyar da za ayi zuwa makarantar.
Ya bayyana yawan yaran da basu zuwa makaranta, ko dai ya kasance ba a sasu makarantar ba,ko kuma sun bar zuwa ne kafin su kai aji uku na Firamare, inda ya ce rashin ilimi a farkon rayuwar yaro ba karamin taimakawa hakan ya yi ba, wajen rashin maida hankali kan tafiya makaranta da kuma iya jure ci gaba da yin hakan.
“Yaran da basu da basu damar hanyar zuwa makaranta ba kashi biyu ne ko dai ya kasance sun bar zuwa makarantar ne da wuri. Alamu sun nuna wadanda suka samu ilimin da farko su ne suke ci gaba da zuwa makarantar, su kammala da kuma ci gaba da fahimtar abinda ake koya masu a makarantar kamar yadda ya ce,” .
Jacob ya yi bayanin cewa kashi 90 na yadda kwakwalwa ta ke bunkasa abin yana faruwa ne kafin shekara ta biyar,wannan yana nufin yadda ake kamar muhimmancin zuba jari tun farkon wajen lamarin da ya shafi koyon wani abu domin tabbatar da ana amfani da hankali wajen samun ilimi ganewa ko fahimta, da yadda za ayi amfani da labarin da aka samu ko sako,ta hanyar yin tunani, sai kuma yadda aka san abin ga kuma hankali. Abin ya hada ayyuka kamar wajen yin tunani, maida hankali,harshe, sai kuma yadda za ayi maganin matsala ta hanyar daukar mataki.
Sai dai kuma duk da haka, ya ce rashin samun hanyar da za a kai ga shi tsarin na ECCDE a Jihohin uku, inda lamarin yara masu zuwa makaranta ya kasance kamar haka Kano na da kashi 35, Katsina 25 Jigawa, ita ma Katsina ta na da kashi 25,suna kuma tattare da matsaloli da suka hada da yawan ‘yan makaranta a cikin azuzuwa, karancin Malamai mata da kuma rashin tsaro.
Har ila yau masanan sun bayyana cewa yayin da Kano take da kasafin kudi da ta ware saboda tsarin ilimi na ECCDE, inda Gizo ke ta shi sakar shi ne yadda ake fitar da kudaden abin ya yi matukar kadan, a shekaru uku da suka gabatar, yayin da Jihohin Jigawa da Katsina su basu dama tsarin ilimin na ECCDE.
A na shi jawabin jami’in ofishinIn his remarks, UNICEF na Kano mai kulawa da irin lamarin, Dakta. Karanbeer Singh,ya bayyana ilimin da ake ba yaro a farkon rayuwar sa a matsayin “abin yana daga cikin babban tsari na kamar zuba jari,” inda ya kara yin bayanin kan yaran da suka samu ilimi a farkon rayuwarsu suna daga cikin wadanda za su samu halin yin nasara a karatunsu da kuma iya zama da al’umma.
Ya yi karin haske na cewa shi lamarin samar da ilimin farkon rayuwa ta yaro ko yara har yanzu yana kara ci baya, inda kashi kusan kashi 29 na yaran ne a Kano, kashi 32 a Katsina yayin da ita kuma Jihar Jigawa aka bar ta da kashi 24 dangane samun galaba kan lamarin na farkon rayuwar yara.
Singh ya yi kira da gwamnatocin Jahohi su kara kudaden da ake kashewa wajen tafiyar da harkokin gida, dauki kwararrun Malaman makarantar, su bunkasa kayan koyo da koyarwa da kuma har ila yau kayan da za su taimakawa Malamai jin dadin koya abubuwan da suke koyarwa.
Da take na ta jawabi lokacin yaron, matar Gwamnan Jihar Jigawa, Hajiya Hadiza Namadi, da Hajiya Kadijat Mohammed,ta wakilce ta yi bayani kan irin matukar kulawar da gwamnati take yi kan lamarin da ya shafi samun damar bada ilimin rayuwar farko ta yaro ko yara, abinda ta yi ma kallon wani babban ginshiki ne na ci gaban kasa da bunkasarta.
Masu ruwa da tsaki a wurin taron sun dauki alkawari na yin duk abinda ya kamata su hada karfi da karfe wajen kara inganta daukar Malaman makaranta, bunkasa abubbuwn more rayuwa wadanda su ma suna daga cikin abubuwan da ke bunkasa shi ilimin,da kuma yin duk abinda ya kamata wajen yadda za a kara yaran da kuma samun sakamako mai inganci na karatun yara a Jihohin uku.















Discussion about this post