• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aboki Mai Natsuwa Shi Ne Wanda Ake Iya Dogaro A Kansa

by Sulaiman and CGTN Hausa
12 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Aboki Mai Natsuwa Shi Ne Wanda Ake Iya Dogaro A Kansa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan da kasar Sin ta kaddamar da manufar yin gyare-gyare a gida da bude kofa ga kasashen waje a shekarar 1978, tattalin arzikin kasar ta fara kama hanyar samun ci gaba cikin sauri. Saboda haka manufar gyare-gyare na da ma’ana mai muhammanci ga kasar.

A kwanan baya, kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin dake rike da ragamar mulki a kasar, ya gudanar da cikakken zaman taronsa na uku, inda aka tsara manufofi masu alaka da tattalin arziki da sauran harkokin mulki, da za a aiwatar da su cikin shekaru fiye da 10 masu zuwa, kana an zartas da kudurin kara zurfafa gyare-gyare, da ingiza aikin zamanantar da kasa ta dabarar musamman ta kasar Sin.

  • Zanga-Zanga Ko Kun San Babban Dalilin Garƙame Abusalma A Kurkuku
  • Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba: Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 9 Duk Shekara – Majalisa

Wannan taro ya nuna dorewar manufofin kasar Sin. A ko da yaushe kasar tana nacewa ga bin hanyar da ta dace da yanayin da take ciki. Kana idan mun kwatanta manufofin da kasar Sin ta gabatar a wajen taron na wannan karo da tarukan da suka gudana a baya, za mu ga yadda kasar ta gaji manufofi na baya, gami da kokarin raya su a kai a kai.

Abu na biyu da taron ya nuna mana shi ne ra’ayin shugabannin kasar Sin na kokarin daukar hakikanan matakai, inda idan an gamu da matsala, to, sai a yi kokarin daidaita ta hanyar yin gyare-gyare. A wajen taron jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin na wannan karo, an gabatar da matakan gyare-gyare fiye da 300, wadanda a cikinsu akwai matakan da aka tsara bisa inganta wasu tsoffin matakai, gami da wasu sabbin matakan da aka kirkira don biyan bukatun daidaita wasu sabbin matsalolin da ake fuskantar. Sa’an nan matakan kasar Sin na daidaita manufofi da yin gyare-gyare sun nuna amfaninsu, har ma sun samu amincewa daga kafofin watsa labaru na Najeriya. Misali, jaridar the Guardians ta kasar Najeriya ta wallafa wani bayani a shafinta ta yanar gizo ta Internet, wanda ya yi kira da a koyi dabarar kasar Sin ta rage talauci. An ce, ta hanyar yi wa tattalin arziki gyare-gyare, da kai dauki ga iyalai masu fama da talauci yadda suke bukata, kasar Sin ta fitar da jama’arta fiye da miliyan 800 daga kangin talauci, adadin da ya kai kashi 75% na al’ummar da aka fid da su daga kangin talauci a duk duniya.

Sa’an nan abu na 3 da wannan taro ya nuna shi ne, maimakon gabatar da manufofi yadda ta ga dama, kasar Sin ta tsara manufofinta ne bayan gudanar da nazari da tattaunawa cikin wani dogon lokaci. Hakika wasu watanni kafin budewar taron na wannan karo, Xi Jinping, babban magatakardan kwamitin koli na jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, ya jagoranci wani taron sauraron ra’ayin kwararru na sassa daban daban, dangane da aikin kula da harkokin kasa, inda ya jaddada bukatar sauraron ra’ayin jama’a bisa abubuwan da suke bukata, da shawarwarin da za su iya gabatarwa, don tabbatar da samar da daidaitattun manufofi.

Labarai Masu Nasaba

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

To, mene ne muhimmancin taron da ya gudana a kasar Sin a wannan karo, ga kasar Najeriya, da sauran kasashen dake nahiyar Afirka?

Da farko, yadda kasar Sin ta tsara manufofi bisa wani daidaitaccen tsari, da kokarin aiwatar da su yadda ake bukata, ya nuna cewa, kasar wata abokiyar hulda ce da ake iya hadin gwiwa da ita cikin dogon lokaci da wani yanayi mai karko. Duk wani matakin da kasar Sin ta dauka, ta tsara shi ne bisa gudanar da bincike na dogon lokaci, da yin tattaunawa tsakanin mutanen sassa daban daban. Saboda haka, babu bukatar damuwa kan rashin dorewar manufofinta, kuma da wuya ne a samu wata manufar da aka tsara cikin kuskure, yayin da ake hadin gwiwa da Sin.

Na biyu shi ne, yadda kasar Sin take kokarin zurfafa gyare-gyare da zamanantar da al’ummarta shi ma zai daga matsayin hadin gwiwarta da Najeriya, gami da sauran kasashen dake nahiyar Afirka baki daya.

Misali, a wajen taron jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin na wannan karo, an gabatar da manufofi na kara bude kofa ga kasashen waje, da kyautata tsarin aiwatar da shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”, da tabbatar da daidaito tsakanin mabambantan kasashe, da dunkule tattalin arzikin duniya waje guda a kokarin tabbatar da moriyar kowace kasa, da dai makamantansu.

Idan an kwatanta da kisan gillar da aka nema yi wa Donald Trump a baya bayan nan, wanda ke takarar neman zama shugaban kasar Amurka, da sauran ayyukan siyasa na kasar Amurka, masu cike da karfin tuwo da tashin hankali, taron da ya gudana a kasar Sin a wannan karo, da sauran ayyukan siyasa na kasar, tamkar “babu gishiri” a cikinsu.

Amma yayin da ake neman abokan hulda, ba za a nemi “masu gishiri” ba, maimakon haka, an fi son zabar abokai da suka san ya kamata, wadanda ke iya daukar hakikanan matakai masu amfani cikin natsuwa. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zanga-Zanga Ko Kun San Babban Dalilin Garƙame Abusalma A Kurkuku

Next Post

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 8 A Lardin Sichuan Na Sin

Related

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
Ra'ayi Riga

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

1 day ago
Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa
Ra'ayi Riga

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

2 days ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

3 days ago
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

1 week ago
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
Ra'ayi Riga

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

2 weeks ago
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Ra'ayi Riga

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

2 weeks ago
Next Post
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 8 A Lardin Sichuan Na Sin

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 8 A Lardin Sichuan Na Sin

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

July 5, 2025
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

July 5, 2025
‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

July 5, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

July 5, 2025
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

July 5, 2025
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

July 5, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

July 5, 2025
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

July 5, 2025
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.