ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aboki Mai Natsuwa Shi Ne Wanda Ake Iya Dogaro A Kansa

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 years ago
Aboki

Tun bayan da kasar Sin ta kaddamar da manufar yin gyare-gyare a gida da bude kofa ga kasashen waje a shekarar 1978, tattalin arzikin kasar ta fara kama hanyar samun ci gaba cikin sauri. Saboda haka manufar gyare-gyare na da ma’ana mai muhammanci ga kasar.

A kwanan baya, kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin dake rike da ragamar mulki a kasar, ya gudanar da cikakken zaman taronsa na uku, inda aka tsara manufofi masu alaka da tattalin arziki da sauran harkokin mulki, da za a aiwatar da su cikin shekaru fiye da 10 masu zuwa, kana an zartas da kudurin kara zurfafa gyare-gyare, da ingiza aikin zamanantar da kasa ta dabarar musamman ta kasar Sin.

  • Zanga-Zanga Ko Kun San Babban Dalilin Garƙame Abusalma A Kurkuku
  • Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba: Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 9 Duk Shekara – Majalisa

Wannan taro ya nuna dorewar manufofin kasar Sin. A ko da yaushe kasar tana nacewa ga bin hanyar da ta dace da yanayin da take ciki. Kana idan mun kwatanta manufofin da kasar Sin ta gabatar a wajen taron na wannan karo da tarukan da suka gudana a baya, za mu ga yadda kasar ta gaji manufofi na baya, gami da kokarin raya su a kai a kai.

ADVERTISEMENT

Abu na biyu da taron ya nuna mana shi ne ra’ayin shugabannin kasar Sin na kokarin daukar hakikanan matakai, inda idan an gamu da matsala, to, sai a yi kokarin daidaita ta hanyar yin gyare-gyare. A wajen taron jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin na wannan karo, an gabatar da matakan gyare-gyare fiye da 300, wadanda a cikinsu akwai matakan da aka tsara bisa inganta wasu tsoffin matakai, gami da wasu sabbin matakan da aka kirkira don biyan bukatun daidaita wasu sabbin matsalolin da ake fuskantar. Sa’an nan matakan kasar Sin na daidaita manufofi da yin gyare-gyare sun nuna amfaninsu, har ma sun samu amincewa daga kafofin watsa labaru na Najeriya. Misali, jaridar the Guardians ta kasar Najeriya ta wallafa wani bayani a shafinta ta yanar gizo ta Internet, wanda ya yi kira da a koyi dabarar kasar Sin ta rage talauci. An ce, ta hanyar yi wa tattalin arziki gyare-gyare, da kai dauki ga iyalai masu fama da talauci yadda suke bukata, kasar Sin ta fitar da jama’arta fiye da miliyan 800 daga kangin talauci, adadin da ya kai kashi 75% na al’ummar da aka fid da su daga kangin talauci a duk duniya.

Sa’an nan abu na 3 da wannan taro ya nuna shi ne, maimakon gabatar da manufofi yadda ta ga dama, kasar Sin ta tsara manufofinta ne bayan gudanar da nazari da tattaunawa cikin wani dogon lokaci. Hakika wasu watanni kafin budewar taron na wannan karo, Xi Jinping, babban magatakardan kwamitin koli na jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, ya jagoranci wani taron sauraron ra’ayin kwararru na sassa daban daban, dangane da aikin kula da harkokin kasa, inda ya jaddada bukatar sauraron ra’ayin jama’a bisa abubuwan da suke bukata, da shawarwarin da za su iya gabatarwa, don tabbatar da samar da daidaitattun manufofi.

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

To, mene ne muhimmancin taron da ya gudana a kasar Sin a wannan karo, ga kasar Najeriya, da sauran kasashen dake nahiyar Afirka?

Da farko, yadda kasar Sin ta tsara manufofi bisa wani daidaitaccen tsari, da kokarin aiwatar da su yadda ake bukata, ya nuna cewa, kasar wata abokiyar hulda ce da ake iya hadin gwiwa da ita cikin dogon lokaci da wani yanayi mai karko. Duk wani matakin da kasar Sin ta dauka, ta tsara shi ne bisa gudanar da bincike na dogon lokaci, da yin tattaunawa tsakanin mutanen sassa daban daban. Saboda haka, babu bukatar damuwa kan rashin dorewar manufofinta, kuma da wuya ne a samu wata manufar da aka tsara cikin kuskure, yayin da ake hadin gwiwa da Sin.

Na biyu shi ne, yadda kasar Sin take kokarin zurfafa gyare-gyare da zamanantar da al’ummarta shi ma zai daga matsayin hadin gwiwarta da Najeriya, gami da sauran kasashen dake nahiyar Afirka baki daya.

Misali, a wajen taron jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin na wannan karo, an gabatar da manufofi na kara bude kofa ga kasashen waje, da kyautata tsarin aiwatar da shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”, da tabbatar da daidaito tsakanin mabambantan kasashe, da dunkule tattalin arzikin duniya waje guda a kokarin tabbatar da moriyar kowace kasa, da dai makamantansu.

Idan an kwatanta da kisan gillar da aka nema yi wa Donald Trump a baya bayan nan, wanda ke takarar neman zama shugaban kasar Amurka, da sauran ayyukan siyasa na kasar Amurka, masu cike da karfin tuwo da tashin hankali, taron da ya gudana a kasar Sin a wannan karo, da sauran ayyukan siyasa na kasar, tamkar “babu gishiri” a cikinsu.

Amma yayin da ake neman abokan hulda, ba za a nemi “masu gishiri” ba, maimakon haka, an fi son zabar abokai da suka san ya kamata, wadanda ke iya daukar hakikanan matakai masu amfani cikin natsuwa. (Bello Wang)

Aboki
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace
  • Sulaiman
    Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum
  • Sulaiman
    Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana
Aboki
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 8 A Lardin Sichuan Na Sin

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 8 A Lardin Sichuan Na Sin

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.