Mutuwar Lumi Elisha Gwamis, wani jami’i a Hukumar Kwastam ta Nijeriya, ta tayar da hankalin mazauna garin Boi da ke ƙaramar hukumar Bogoro a Jihar Bauchi.
Gwamis mai shekaru 44, ɗan tsohon shugaban ƙaramar hukumar Bogoro, Hon. Elisha Tula Gwamis ne.
Wasu rahotanni daga yankin sun yi zargin cewa marigayin yana fama da matsananciyar damuwa kafin rasuwarsa, inda ake zargin ita ce sanadin kashe kansa.
Amma mahaifinsa ya ce ɗansa yana cikin ƙoshin lafiya kafin abin ya faru, kuma ya bayyana lamarin a matsayin abin baƙin ciki da mamaki.
Ita ma Hukumar Kwastam, sashen FOU D na Bauchi, ta musanta zargin kashe kansa.
Kakakin hukumar, Umar Abdullahi, ya ce babu wata hujja da ta tabbatar da hakan.
Ya ce marigayin ya je ofishinsu tare da mahaifinsa domin kammala cike wasu takardu bayan an tura shi sabon wajen aiki daga Tin Can Island.
Daga nan ya tafi hutun shekara kafin daga bisani aka sanar da mutuwarsa.
Hukumar ta ce tana jiran cikakken bincike don gano musabbabin rasuwarsa.
Za a yi jana’izarsa a ranar Laraba, 10 ga watan Yuni, a garin Boi.














Discussion about this post