Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya musanta rahotannin da ke cewa yana dab da ficewa daga ADC zuwa wata jam’iyya daban, yana mai cewa har yanzu bai yanke wani hukunci na ƙarshe ba game da makomarsa ta siyasa.
A cikin wata sanarwa da ya fitar domin mayar da martani kan abin da ya kira “labarai masu ruɗarwa” da ke yawo a bainar jama’a, Kwankwaso ya ce tattaunawar da ake yi kan yiwuwar sauyin sheƙa a cikin jam’iyyar sakamakon rikicin da take fuskanta ta yi wuri.
“Mun lura da rahotannin kafafen yaɗa labarai da tattaunawa da ke nuna yiwuwar sauyin sheƙa a cikin ADC saboda matsalolin da jam’iyyar ke fuskanta,” in ji shi.
“Dangane da waɗannan bayanai masu ruɗani da ke yawo, ina bayyana karara cewa har yanzu ba a yanke wani hukunci na ƙarshe ba dangane da makomata ta siyasa ko ta abokan tafiyata.”
Sai dai Kwankwaso ya nuna cewa wasu sabbin hukuncin kotu da suka shafi jam’iyyar sun ƙara jefa ta cikin rashin tabbas, ciki har da hukuncin Kotun Koli na kwanan nan wanda, a cewarsa, ya tabbatar da halascin Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa (NWC) ƙarƙashin jagorancin David Mark, amma ya mayar da shari’ar zuwa babbar kotu domin ci gaba da sauraro.
“Sabon hukuncin Kotun Ƙoli, duk da cewa ya tabbatar da halascin NWC ƙarƙashin David Mark, ya kuma mayar da shari’ar zuwa Babbar Kotu. Wannan ya sanya jam’iyyar cikin mawuyacin hali,” in ji shi.
Ya kuma bayyana cewa, hukuncin Babbar Kotun Tarayyar a baya ya soke babban taron jam’iyyar na baya-bayan nan, sannan kuma, akwai wani yunƙuri na daban daga Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya (AGF) na neman soke rijistar ADC, duk waɗannan batutuwan sun ƙara dagula al’amuran jam’iyyar.














Discussion about this post