Tawagar kasar Sin ta mika takarda mai dauke da matsayinta mai taken “Takardar Matsayin Kasar Sin kan Shugabancin Intanet a Zamanin Fasahohin Zamani.” Biyo bayan yadda take mayar da hankali kan ‘yancin intanet, a wannan karon, kasar Sin ta gabatar da muhimmiyar ka’ida kan ‘yancin fasahar dijital, wadda ke wakiltar matakinta na baya- bayan nan na aiwatar da shawarwarin inganta shugabancin duniya da na gina al’umma mai makoma ta bai daya a fannin intanet.
Kasar Sin ta mika takardar ce yayin taro na farko na tsarin dindindin kan tsaron intanet na duniya na MDD wanda ke gudana a hedkwatar majalisar daga ranar 20 zuwa 24 ga wata.Takardar ta jaddada cewa, domin samun zaman lafiya da kwanciyar hankali, ya kamata dukkan kasashe su yi biyayya ga manufofi da ka’idojin kundin tsarin mulkin MDD kan intanet, wanda ke kira da mutunta ‘yancin amfani da fasahohin dijital da ci gaba na bai daya, tana mai cewa dukkan kasashe na da ‘yancin zabar hanyoyin raya fasahohin zamani, ciki har fasahar AI, bisa yanayin da ya dace da su, kuma suna da ‘yancin zabar fasahohi da kayayyaki da hidimomin AI da suke so, kuma bai kamata a tilasta musu goyon bayan wani bangare ba.
Ta kuma nanata bukatar nace wa tsarin cudanyar bangarori da dama, da shawo kan barazanar da fasahohi masu bullowa kamar AI ke yi ga tsaron intanet da kuma tsara sabbin dokokin intanet na duniya a kan lokaci.
Shugaban tawagar kasar Sin kuma shugaban kula da harkokin da suka shafi intanet da fasahohin zamani a ma’aikatar kula da harkokin wajen kasar Sin ne ya gabatar da takardar matsayin kasar Sin yayin taron na duniya (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)














