Mataimakiyar Shugabar Matan Jam’iyyar PDP ta Jihar Kano, Hajiya Khadija Ɗahiru Gama ta bayyana cewa, PDP na ƙara ƙoƙari wajen tuntuɓar mata a lungu da saƙo na Jihar Kano domin wayar musu da kai kan halin da ƙasar nan ta shiga da kuma yadda jam’iyyar ta shirya domin tabbatar da samar da farin ciki da walwala ga mata da matasa a faɗin ƙasar baki ɗaya idan ta kafa gwamnati.
Hajiya Khadija ta bayyana hakan ne a Jihar Kano. Ta ce akwai abubuwa masu muhimmanci da mata da al’ummar ƙasar nan baki ɗaya ya kamata su tuna da su a lokacin da PDP ke mulki.
“A lokacin mulkin PDP, ƙasar nan na cikin kwanciyar hankali da walwala da sauƙin rayuwa da samun ilimi mai inganci da kyautatata harkar lafiya. Amma a yanzu duk waɗannan abubuwa babu kowa yana cikin ruɗani a kowane ɓangare,”in ji ta.
Hajiya Khadija ta yi nuni da cewa ba sai an gaya wa ƴan Nijeriya jam’iyyar da za su zaɓa ba, domin PDP ita ce hanya kawai ta kawo gyara. Ta nuna damuwarta kan yadda rashin tsaro ya ƙaru, kamar yadda ake faɗan daba da rana tsaka a Kano, ana kisan kai ba wani mataki da ake ɗauka, sannan kuma harkar ilimi ya taɓarɓare.
“Mu iyaye mata ba ma jin daɗin ganin ƴaƴanmu ba sa samun ilimi. Domin ilimi shi ne tushen tarbiyya. Amma a yanzu aji ɗaya za ka samu a cushe ɗalibai sama da 200 a ciki, wanda a ƙa’idar koyarwa ba haka ba ne. Babu abin da yaro zai fahimta a irin wannan yanayi. Wannan yana matuƙar damun mata a Kano da Nijeriya baki ɗaya,” in ji ta.














