Jam’iyyar ADC ta rubuta wa Babbar Alƙalin Nijeriya (CJN), inda ta roƙi a hanzarta yanke hukunci kan ƙarar da ke gaban Kotun Ƙoli dangane da rikicin shugabanci da ke addabar jam’iyyar.
A cikin wasiƙar da aka rubuta ranar 28 ga Afrilu, 2026, jam’iyyar ta hannun lauyoyinta ta bayyana buƙatar gaggawa domin kauce wa illa ga shirin ta na shiga zaɓen 2027.
Rahotanni sun nuna cewa ƙarar na da alaƙa da takaddamar shugabanci tsakanin ɓangaren David Mark da kuma na Nafiu Bala Gombe tare da wasu.
Jam’iyyar ta bayyana cewa Kotun Ƙoli ta riga ta saurari ƙarar a ranar 22 ga Afrilu, inda ta ajiye hukunci, amma har yanzu ba a bayyana ranar yanke hukuncin ba.
A cikin wasiƙar, lauyoyin ADC sun jaddada cewa jinkirin yanke hukunci na iya haifar da mummunar illa ga tsarin jam’iyyar, musamman dangane da sahihancin shugabancinta.
Sun ce hukuncin kotunan da suka gabata ya janyo rashin tantance sahihin shugabancin jam’iyyar, lamarin da ya haifar da ruɗani kan wanda ke da ikon wakiltar ADC a hukumance.
Haka kuma sun bayyana damuwa cewa INEC na iya ɗaukar matakai bisa hukuncin da ake da shi a halin yanzu, wanda ka iya ƙara dagula lamarin idan ba a yanke hukunci cikin gaggawa ba.
Lauyoyin sun gargadi cewa idan aka ci gaba da jinkiri, akwai yiwuwar ADC ta rasa damar shiga zaɓen 2027, saboda cika wa’adin tsarin zaɓe.
Sun ƙara da cewa hakan zai iya tauye haƙƙin miliyoyin ’yan Nijeriya da ke goyon bayan jam’iyyar wajen shiga harkokin siyasa.
Duk da amincewa da cunkoson aiki da ke gaban Kotun Ƙoli, sun roƙi Babbar Alƙali da ta sa baki domin tabbatar da cewa an yanke hukunci cikin gaggawa, suna mai jaddada cewa “jinkirin adalci, tauye adalci ne.”















Discussion about this post