ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ADC Ta Nemi Kotu Ta Hanzarta Yanke Hukunci Kan Rikicin Shugabancin Jam’iyyar

by Muhammad
1 month ago

Jam’iyyar ADC ta rubuta wa Babbar Alƙalin Nijeriya (CJN), inda ta roƙi a hanzarta yanke hukunci kan ƙarar da ke gaban Kotun Ƙoli dangane da rikicin shugabanci da ke addabar jam’iyyar.

A cikin wasiƙar da aka rubuta ranar 28 ga Afrilu, 2026, jam’iyyar ta hannun lauyoyinta ta bayyana buƙatar gaggawa domin kauce wa illa ga shirin ta na shiga zaɓen 2027.

Rahotanni sun nuna cewa ƙarar na da alaƙa da takaddamar shugabanci tsakanin ɓangaren David Mark da kuma na Nafiu Bala Gombe tare da wasu.

ADVERTISEMENT

Jam’iyyar ta bayyana cewa Kotun Ƙoli ta riga ta saurari ƙarar a ranar 22 ga Afrilu, inda ta ajiye hukunci, amma har yanzu ba a bayyana ranar yanke hukuncin ba.

A cikin wasiƙar, lauyoyin ADC sun jaddada cewa jinkirin yanke hukunci na iya haifar da mummunar illa ga tsarin jam’iyyar, musamman dangane da sahihancin shugabancinta.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Sun ce hukuncin kotunan da suka gabata ya janyo rashin tantance sahihin shugabancin jam’iyyar, lamarin da ya haifar da ruɗani kan wanda ke da ikon wakiltar ADC a hukumance.

Haka kuma sun bayyana damuwa cewa INEC na iya ɗaukar matakai bisa hukuncin da ake da shi a halin yanzu, wanda ka iya ƙara dagula lamarin idan ba a yanke hukunci cikin gaggawa ba.

Lauyoyin sun gargadi cewa idan aka ci gaba da jinkiri, akwai yiwuwar ADC ta rasa damar shiga zaɓen 2027, saboda cika wa’adin tsarin zaɓe.

Sun ƙara da cewa hakan zai iya tauye haƙƙin miliyoyin ’yan Nijeriya da ke goyon bayan jam’iyyar wajen shiga harkokin siyasa.

Duk da amincewa da cunkoson aiki da ke gaban Kotun Ƙoli, sun roƙi Babbar Alƙali da ta sa baki domin tabbatar da cewa an yanke hukunci cikin gaggawa, suna mai jaddada cewa “jinkirin adalci, tauye adalci ne.”

Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Wakilin Sin: Matsalolin Mashigin Hormuz Sun Samo Asali Ne Daga Ayyukan Soji Da Amurka Da Isra’ila Suka Kaddamar Kan Iran

Wakilin Sin: Matsalolin Mashigin Hormuz Sun Samo Asali Ne Daga Ayyukan Soji Da Amurka Da Isra'ila Suka Kaddamar Kan Iran

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.