ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Afirka Na Da Wata Abokiya Da Za Ta Iya Dogaro Da Ita

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Afirka

Idan a dab da kai akwai wani, wanda yake da sanin kamata, da kwarewar aiki, da son cika alkawari, kana yayin da yake hulda da sauran mutane, yana da natsuwa, da kulawa da moriyar su, toh ganin kana da irin wannan mutumin kirki da za a iya dogaro da shi, ba zai sa ka yi sha’awar kulla abokantaka da shi ba?

Hakika, kasar Sin abokiyar kasashen Afirka ce, wadda halayyarta ta yi kama da ta wannan mutumin da na ba da misali.

  • Eric Chelle Ya Sake Bai Wa Ahmed Musa Damar Taka Leda A Super Eagles
  • Azumin Ramadan: Gwamna Buni Ya Amince Da Naira Miliyan 297 Don Ciyar Da Mutane 51,000 A Kullum

A wajen taron shekara-shekara na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin, da aka kaddamar da shi yau a birnin Beijing na kasar, firaministan kasar Sin Li Qiang ya gabatar da rahoton ayyukan gwamnati, wanda ya shaida mana yanayin tabbas da Sin take da shi daga bangarori 2:

ADVERTISEMENT

Na farko, yadda ake samun tabbaci kan ci gaban tattalin arzkin Sin.

Idan an lura da yanayin tattalin arzikin kasar Sin, to, za a san cewa har kullum gwamnatin kasar ta kan cika alkawuran da ta yi a fannin raya tattalin arziki. Kamar yadda alkaluma daga cikin rahoton aikin gwamnatin Sin suka nuna: An yi hasashen samun karuwar GDPn kasar da ta kai kimanin kaso 5% a shekarar 2024, daga baya matsayin karuwar da ta cimma shi ne kaso 5%. Kana an yi hasashen samun sabbin guraben aikin yi fiye da miliyan 12 a birane da garuruwan kasar, a shekarar 2024, yayin da jimilla ta hakika ita ce miliyan 12.56. Haka zalika, an yi hasashen girbin hatsi fiye da kilo biliyan 650 a kasar a bara, yayin da yawan hatsin da aka samu a karshe ya kai fiye da kilo biliyan 700. Kana kasar ta kiyaye wani yanayi na samun ci gaba mai armashi a dukkan bangarorin da suka hada da ciniki, da masana’antu, da kare muhalli, da dai sauransu. To, wannan yanayin da kasar ke ciki na samun tabbaci kan ci gaban tattalin arzikinta ya ba ta damar cika duk wani burin da ta sanya a gaba.

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

Na biyu, shi ne dorewar manufofin kasar Sin.

Za a iya ganin dorewar manofofin Sin, bisa tantance rahotannin aikin gwamnatinta na shekaru daban daban. Misali, a cikin rahoto na wannan karo, an ambaci manufofin raya shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”, da habaka cudanyar kasa da kasa a fannin al’adu, da tsayawa kan niyyar amfanawa juna yayin da ake hadin gwiwa da sauran kasashe, da dai sauransu. Sai dai dukkansu tsoffin manufofin kasar Sin ne da ake ci gaba da kokarin aiwatar da su. Hakan ya nuna cewa, manufofin Sin a fannin diplamasiyya, musamman ma ta fuskar hulda da kasashen Afirka, su ma suna cikin wani yanayi na tabbas. Kamar yadda ministan wajen kasar Sin ya kan ziyarci kasashen Afirka a farkon duk wata sabuwar shekara, cikin wasu shekaru 35 a jere, ya nuna cewa kulla abokantaka da kasashen Afirka wata manufa ce ta tushe da kasar Sin take kokarin tsayawa a kanta.

To, wadannan fannoni 2 da na ambata sun tabbatar da sakamakon hadin gwiwar Sin da Afirka mai armashi.

Misali, kasar Sin ta dade da kasancewa kasar da ta fi yawan ciniki da kasashen Afirka, kana jimillar cinikinsu na ta samun karuwa. A shekarar 2024, darajar kayayyakin da aka yi cinikinsu tsakanin Sin da Afirka ta kai kimanin dalar Amurka biliyan 289.1, adadin da ya karu da kaso 6.1% bisa na shekarar 2023. Kana a bangaren zuba jari, yawan kudin da kamfanonin Sin suka zubawa kasuwannin Afirka ya kai fiye da dala biliyan 40 a karshen shekarar 2023. Yayin da a Najeriya, shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” da kasar Sin ta gabatar tun shekarar 2013 ta riga ta haifar da ayyukan raya kasa fiye da 3000, inda ko a cikin watanni 2 da suka gabata ma, an ga yadda wani kamfanin Sin ya kammala aikin gyara da habaka manyan titunan da suka hada Keffi da Makurdi, kana bangarorin Sin da Najeriya sun kulla yarjejeniyar kafa babbar masana’antar samar da iskar Hydrogen ta zafin hasken rana a jihar Akwa Ibom.

Hakika idan mun duba muhallin duniya, za mu ga yadda ya cika da yanayin rashin tabbas. Wanda ya samo asali daga yake-yake, da bala’u daga Indallahi, gami da canzawar ra’ayi da wasu kasashen su kan yi, misali, a jiya sun ba ka tallafi, sa’an nan yau suka dakatar da shi, toh watakila gobe ma za su bukaci ka mayar musu kudinsu. To, yayin da ake fuskantar wannan muhalli, abu ne mai kyau a samu wani aboki da za a iya dogaro da shi. Abun haka yake ko? (Bello Wang)

Afirka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Halarci Bitar Tawagar Lardin Jiangsu

Xi Jinping Ya Halarci Bitar Tawagar Lardin Jiangsu

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.