Fitacciyar ‘yar gwagwarmaya, Aisha Yesufu, ta sanar da ficewarta daga jam’iyyar ADC tare da komawarta Jam’iyyar NDC.
Haka kuma, ta bayyana aniyarta ta tsayawa takarar kujerar Sanata mai wakiltar Babban Birnin Tarayya (FCT) a zaɓen 2027.
Yesufu ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X, inda ta ce matakin nata ya biyo bayan abin da ta kira “fahimta mai zurfi game da makomar ƙasa,” tare da jaddada cewa tana tafiya ne da akidar siyasar Peter Obi.
A cewarta: “Kwanaki kaɗan masu zuwa za su tantance makomar wannan ƙasa. Wannan fahimtar ce ta sa na fice daga ADC na koma NDC, domin ina bin jagorancin Mai Girma Peter Obi, wanda a yau yake wakiltar fata da burin Nijeriya mai haske.”
Wannan mataki na Yesufu na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da sauye-sauyen siyasa da sauyin sheƙa tsakanin ‘yan siyasa gabanin babban zaɓen 2027.















Discussion about this post