• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alakar Gwarzon Dan Kwallo Pele Da Afirka

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
in Wasanni
0
Alakar Gwarzon Dan Kwallo Pele Da Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Talatar data gabata ne dai aka binne gawar shahararren dan wasan kwallon kafar nan na duniya, Pele, wanda ya mutu a ranar Alhamis ta satin da ya gabata yana da shekara 82 a duniya.

Dubban masu makoki ne suka hallara a filin wasan Santos na Brazil, domin ganawa da gawar tsohon dan wasan duniyar kuma an ajiye gawar Pele a tsakiyar filin Urbano Caldiera da ke Sao Paulo, yayin da magoya baya suka yi dogon layi suna tozali da ita.
Tsohon dan wasan wanda ya kafa tarihin cin kofin duniya sau uku a tarihi, ya mutu ne bayan ya sha fama da jinya wadda ya dade yanayi kuma a wasu lokuta a baya ma aka dinga yada jita-jitar cewa ya mutu.

  • Dan Wasan Duniya, Pele, Ya Rasu Yana Da Shekaru 82

Daga cikin manyan bakin da suka halarci jana’izar akwai shugaban hukumar kwallon kafa ta duniya, Gianni Infantino, wanda ya ce za su bukaci kowace kasa a duniya ta saka sunan Pele a daya daga cikin filayenta.

Kasancewar Pele daya daga cikin manyan taurarin matasan bakaken fata a fagen wasanni a zamanin talabijin, Pelé ya samu karbuwa da kauna daga ‘yan Afirka a fadin nahiyar gaba daya.

A lokacin da kasashen Afirka ke fafutukar samun ‘yancin- kai a karshe-karshen shekarun 1950 da kuma farko-farkon shekarar 1960, Pelé ya dinga samun gayyata daga kasashen Afirka da suka samu ‘yanci, domin wasan sada zumunta da kungiyar sa ta Santos FC da kuma tawagar kasar sa ta Brazil.

Labarai Masu Nasaba

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique

A tarihin sa da ya rubuta, Pelé ya bayyana cewa wadannan tafiye-tafiye da ya yi zuwa kasashen Afirka a wannan lokaci ba kawai sun sauya yadda yake kallon duniya ba har ma da yadda ya ce duniya ta dauke shi.

Mutumin da ya rubuta kundin kungiyar kwallon kafa ta Santos, Guilherme Nascimento, ya yi daidai kamar yadda ya nuna cewa wadannan tafiye-tafiye zuwa Afirka na cike da labarai wadanda kusan da wuya a iya bambancewa tsakanin na gaskiya da kuma na kunne-ya-girmi-kaka.

A misali, zuwan Pelé Algeria, ya kasance kamar wani abu na fim. A shekarar 1965, tauraron wanda a lokacin yana da shekara 24 ya je kasar a daidai lokacin da darektan fim, Gillo Pontecorbo yake hada fim din ”The Battle of Algiers”.

A kan haka sai abin ya zo daidai da lokacin da za ka ga tankokin yaki suna ta kai-komo a fadin kasar kama daga kauyuka zuwa Casbah sannan shugaban kasar na wancan lokaci Ahmed Ben Bella, mai matukar sha’awar wasan kwallon kafa ya shirya wasan sada zumunta biyu domin wannan ziyara.

Sai dai kuma ministan tsaro na lokacin Houari Boumediene ya yi juiyin mulki inda ya hambarar da Shugaba Ben Bella, saboda haka ya soke daya wasan sada zumuntar wasu ‘yan jarida da masu fashin baki sun ce ministan ya yi amfani da yanayin da ake ciki na ruguguguwa da murnar zuwan tauraron kwalon kafar, a matsayin wata hanya ta dauke hankali ya yi juyin mulkin.

Sai dai tarin ziyarar da Pele ya dinga kaiwa Moroko a matsayin sa na tauraron kwallon kafa a lokacin ba su kai kamar na wasu ba sannan an ce ya yi wasu kalamai masu dadadawa da yabo ga tawagar kasar da ta je gasar cin Kofin Duniya a 1970 a Medico, kasancewar ita ce kasa ta farko a Afirka da ta fara samun gurbin wannan gasa ta duniya tun bayan Masar a 1934.

A lokacin wata ziyarar kuma an ce Pele ya yi magana a kan tauraron kwallon kafar kasar ta Moroko na zamanin wato Larbi Ben Barek, wanda ya buga wasa a kungiyoyin Olympikue de Marseille da Atletico Madrid.

Ziyarar Pele zuwa Najeriya da kuma Jamhuriyar Dumukuradiyyar Kongo ita ma ta kasance cike da labarai iri-iri ko dai na gaskiya ko kuma na kanzon-kurege a lokacin zuwansa kasashen biyu an ce ya sa an samu dakatar da bude wuta a kasashen masu karcar bakuncinsa yakin basasa da suke yi.

An yi yakin basasar Najeriya daga shekarar 1967 zuwa 1970, amma duk da haka ana cewa lokacin da ya je domin wani wasa na karramawa da tawagar kwllon Najeriya, an dakatar da bude wuta a yakin tsawon sa’a 48.

Sai dai Pelen da kansa a littafin sa ya rubuta cewa, ba shi da tabbacin cewa lalle gaskiya ne amma ya kara da cewa ‘yan Najeriyar lalle sun dauki matakan tabbatar da cewa ‘yan Biyafara ba su mamayi Lagos ba a lokacin da suke can, yana mai tuna irin tarin sojojin da aka baza a birnin.

Ana wannan magana ce kuwa duk da cewa fa ba ta yadda ‘yan awaren na Biyafara za su iya yin hakan domin suna nisan akalla kilomita 500 ne tsakaninsu da Lagos, hasali ma sojojin Najeriya suna tura su baya a lokacin.

A shekarar 1976, kamfanin lemon kwalba na Amurka, Pepsi ya yi amfani da farin jinin Pele a nahiyar Afirka wajen tallata lemon, inda ya dauki nauyin ziyarar tauraron zuwa Afirka ta Gabas, a kasashen Kenya da Uganda.

A lokacin Sarkin kwallon kamar yadda ake masa lakabi ya yi nasarar tallata lemon tare da gudanar da wasu sansanoni na matasan ‘yan wasa a kasashen biyu. Sannan a Kenya ‘yan kallo sun bayar da murfin kwalbar lemon kafin su shiga kallo, inda manya suke bayar da shida yara kuma uku.

A duk tsawon wadannan shekaru, Pelé ya kuma ziyarci kasashen Mozambikue da Masar da Sudan da Senegal da kuma Ghana sannan bayan ziyarce-ziyarcen masu tarihi, Pelé ya kasance wata alama ta karfafa guiwa da zama abin koyi ga ‘yan kwallon kafa masu tasowa a nan nahiyar Afirka.

Darajar Pele a duniya ce tasa daya daga cikin fitattu kuma manyan gwarazan ‘yan kwallon kafa na Ghana, ya lakaba suna Pele a cikin sunan sa inda ake kiransa da Abedi “Pele” Ayew inda ya ce daukakarsa ta karfafa masa guiwa, wanda hakan ya sa ya dauki sunasan Pele ya yi lakabi da shi domin ya zama kamar sa a tsawon rayuwarsa ta kwallon kafa, har ma bayanta, wanda wannan ba karamar daraja ba ce.

Har kullum Pelé ya kasance mai kyakkyawan fata da kishin ci-gaban Afirka a gasar Kofin Duniya kuma hasashen da ya yi a tsakiyar shekarun 1970 cewa wata kasar Afirka za ta ci Kofin Duniya kafin shekara ta 2000, ya kasance abin tattauna wa sosai kafin fara duk wata gasa ta Kofin Duniya tun daga lokacin da ya yi furucin.

Saboda haka abu ne da ya yi daidai kasancewar sakonninsa na karshe a shafukan internet sun hada da na taya murna da ya yi ga kasar Moroko kan rawar da ta taka ta a-zo-a-gani wadda ta kasance tarihi a gasar Kofin Duniy da aka yi a Katar.

A jawabin sa a shafinsa na twitter akan tawagar kasar Moroko, Pele ya ce “Ba zan kasa taya Moroko murna ba a kan gagarumin kokarin da suka yi kuma abin alfahari ne a ga Afirka ta yi fice.” Kamar yadda ya rubuta a sakon.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Chadi Ta Dakile Yunkurin Juyin Mulki Tare Da Kame Wadanda Suka Kitsa

Next Post

An Tsaurara Tsaro Gabanin Ziyarar Buhari A Adamawa

Related

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana
Wasanni

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

1 day ago
Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique
Wasanni

Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique

3 days ago
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense
Wasanni

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

3 days ago
Ahmed Musa Ya Ƙaryata Kyautar Motoci Ga Ƴan Wasa Da Ma’aikatan Kano Pillars
Wasanni

Ahmed Musa Ya Ƙaryata Kyautar Motoci Ga Ƴan Wasa Da Ma’aikatan Kano Pillars

4 days ago
Zan Yi Ƙoƙarin Dawo Da Martabar Kano Pillars A Idon Duniya — Ahmed Musa
Wasanni

Zan Yi Ƙoƙarin Dawo Da Martabar Kano Pillars A Idon Duniya — Ahmed Musa

4 days ago
Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin
Wasanni

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

4 days ago
Next Post
An Tsaurara Tsaro Gabanin Ziyarar Buhari A Adamawa

An Tsaurara Tsaro Gabanin Ziyarar Buhari A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.