ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Nijeriya Tana Fatan Zuwa Kofin Duniya Na 2026

by Abba Ibrahim Wada
5 months ago
Nijeriya

Har yanzu ana zaman rashin tabbas, yayin da masoya ƙwallon ƙafa a Nijeriya ke jiran hukuncin da hukumar ƙwallon ƙafa ta duniya FIFA za ta yanke kan ƙorafin da Nijeriya ta shigar kan zargin DR Congo da yin amfani da Ƴan wasan da ba su kamata ba a wasannin neman gurbin gasar cin kofin duniya ta 2026.

Tawagar Congo ta cire Nijeriya ne a bugun fenariti a watan Nuwamba domin samun gurbi a wasannin neman gurbi na duniya da za a buga. Amma kuma a cikin watan Disamba Nijeriya ta shigar da ƙorafi, inda ta zargin tawagar Congo da yin amfani da Ƴan wasa Aaron Wan-Bissaka da Aɗel Tuanzebe – waɗanda dukkanin su sun taɓa buga wa Ingila wasa a tawagar matasa, inda Nijeriya ta ce ba su cancanta ba domin dokar ƙasar Congo ba ta amince da Ƴanwasa da suke da takardar zama ɗan ƙasa na ƙasashe biyu ba

  • Sharuɗan Da Chelle Ya Gindaya Wa NFF Domin Cigaba Da Jagorantar Super Eagles 
  • AFCON 2025: Dalilin Da Ya Sa Super Eagles Ba Ta Jira Bikin Karɓar Kyautar Tagulla Ba – NFF

Yayin da wani sashe na magoya bayan tawagar Nijeriya ke fatan ganin ƙasar ta samu wata damar, wasu kuma na ganin cewa tamkar babu adalci idan aka bai wa Nijeriya dama a kan DR Congo. FIFA ta tabbatar da cewa tana nazari kan ƙorafin, to amma ba ta sanar da ranar da za ta yi nazari ko kuma sanar da hukuncin da ta yanke ba, kuma tuni hukumar kula da ƙwallon ƙafa ta Nijeriya – NFF – ta musanta raɗe-raɗin cewa an yi watsi da ƙorafin nata.

ADVERTISEMENT

Babban daraktan yaɗa labaran hukumar ƙwallon ƙafa ta ƙasa Demola Olajire ya bayyana cewa duk wani batu da ke cewa an yanke hukunci ba gaskiya ba ne. Ya ƙara da cewa FIFA ba ta faɗa wa Nijeriya ko hukumar ƙwallon ƙafa ta Congo game da wani hukunci ba.

A lokacin da Nijeriya ta shigar da ƙorafi, shugaban NFF Mohammed Sanusi ya zargi DR Congo da karya dokokin FIFA.

LABARAI MASU NASABA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Bayan wasannin neman gurbi, Tuanzebe da Wan-Bissaka sun kuma buga wa tawagar DR Congo a gasar cin kofin Afirka ta 2025 a Moroko. Amma kuma dokar ƙasar Congo ta ce ɗan wasa ba zai zamo mai takardar zama ɗan ƙasa biyu ba, amma wasu daga cikin Ƴan wasansu na da fasfo na ƙasashen Turai da kuma Faransa.

Tawagar Congo za ta kara da ko dai ƙasar New Caledonia ko Jamaica a karawar da za yi ta wasannin neman gurbi tsakanin ƙasashen duniya a watan Maris. Wanda ya yi nasara a wasan zai shiga cikin jerin ƙasashe 48 da za su buga gasar kofin duniya, a rukunin K, tare da ƙasashen Portugal da Uzbekistan da kuma Colombia.

 

Hukuncin Da Ake Sa Ran FIFA Za Ta Yanke

Kora: Idan FIFA ta yanke hukuncin cewa dalilan Nijeriya ba su da ƙarfi za ta iya watsi da ƙorafin, ta kuma ƙyale DR Congo ta ci gaba da wasan neman gurbin gasar cin kofin duniya.

Bincike da yin hukunci: FIFA za ta iya yin bincike game da ƙorafin, idan ta gano cewa akwai saɓa ƙa’ida wajen tantance Ƴan wasa, za ta hukunta hukumar (ta hanyar cin tara ko gargaɗi) ba tare da sauya sakamako ba.

Yin hukunci: Idan abin ya yi ƙamari, FIFA ko kuma Hukumar ƙwallon ƙafa ta Afirka za su iya sokewa ko kuma ƙwace maki daga mai laifi a miƙa wa mai ƙorafi ko kuma a cire wa ƙasar maki daga cikin wasannin da aka yi na cikin rukuni. A baya, akan yi wannan hukunci ne idan aka gano ƙarara cewa an take doka, ko dai ta hanyar bayar da bayanan ƙarya ko kuma sauya wasu bayanai.

Duk da cewa Nijeriya ta lashe lambar tagulla a gasar cin kofin Afirka ta 2025, wanda ya sanya ta ƙara ɗabbaƙa kanta a matsayin ɗaya daga cikin ƙasashen da suka gawurta a ɓangaren ƙwallon ƙafa a nahiyar, amma abin da ya fito fili shi ne, a halin yanzu, Nijeriya ba za ta je gasar cin kofin duniya ba, in dai ba wani abu ya sauya ba.

Nijeriya
Abba Ibrahim Wada
+ postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Mece Ce Matsalar Real Madrid? 
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Ko Ka San Dalilin Da Zai Bai Wa Nijeriya Damar Zuwa Gasar Cin Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

MASU ALAKA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Wasanni

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Next Post
Siyasar Kano: Akwai Buƙatar Gwamna Abba Ya Ƙara Nazari

Siyasar Kano: Akwai Buƙatar Gwamna Abba Ya Ƙara Nazari

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.