ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Nijeriya Tana Fatan Zuwa Kofin Duniya Na 2026

by Abba Ibrahim Wada
6 months ago
Nijeriya

Har yanzu ana zaman rashin tabbas, yayin da masoya ƙwallon ƙafa a Nijeriya ke jiran hukuncin da hukumar ƙwallon ƙafa ta duniya FIFA za ta yanke kan ƙorafin da Nijeriya ta shigar kan zargin DR Congo da yin amfani da Ƴan wasan da ba su kamata ba a wasannin neman gurbin gasar cin kofin duniya ta 2026.

Tawagar Congo ta cire Nijeriya ne a bugun fenariti a watan Nuwamba domin samun gurbi a wasannin neman gurbi na duniya da za a buga. Amma kuma a cikin watan Disamba Nijeriya ta shigar da ƙorafi, inda ta zargin tawagar Congo da yin amfani da Ƴan wasa Aaron Wan-Bissaka da Aɗel Tuanzebe – waɗanda dukkanin su sun taɓa buga wa Ingila wasa a tawagar matasa, inda Nijeriya ta ce ba su cancanta ba domin dokar ƙasar Congo ba ta amince da Ƴanwasa da suke da takardar zama ɗan ƙasa na ƙasashe biyu ba

  • Sharuɗan Da Chelle Ya Gindaya Wa NFF Domin Cigaba Da Jagorantar Super Eagles 
  • AFCON 2025: Dalilin Da Ya Sa Super Eagles Ba Ta Jira Bikin Karɓar Kyautar Tagulla Ba – NFF

Yayin da wani sashe na magoya bayan tawagar Nijeriya ke fatan ganin ƙasar ta samu wata damar, wasu kuma na ganin cewa tamkar babu adalci idan aka bai wa Nijeriya dama a kan DR Congo. FIFA ta tabbatar da cewa tana nazari kan ƙorafin, to amma ba ta sanar da ranar da za ta yi nazari ko kuma sanar da hukuncin da ta yanke ba, kuma tuni hukumar kula da ƙwallon ƙafa ta Nijeriya – NFF – ta musanta raɗe-raɗin cewa an yi watsi da ƙorafin nata.

ADVERTISEMENT

Babban daraktan yaɗa labaran hukumar ƙwallon ƙafa ta ƙasa Demola Olajire ya bayyana cewa duk wani batu da ke cewa an yanke hukunci ba gaskiya ba ne. Ya ƙara da cewa FIFA ba ta faɗa wa Nijeriya ko hukumar ƙwallon ƙafa ta Congo game da wani hukunci ba.

A lokacin da Nijeriya ta shigar da ƙorafi, shugaban NFF Mohammed Sanusi ya zargi DR Congo da karya dokokin FIFA.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

Bayan wasannin neman gurbi, Tuanzebe da Wan-Bissaka sun kuma buga wa tawagar DR Congo a gasar cin kofin Afirka ta 2025 a Moroko. Amma kuma dokar ƙasar Congo ta ce ɗan wasa ba zai zamo mai takardar zama ɗan ƙasa biyu ba, amma wasu daga cikin Ƴan wasansu na da fasfo na ƙasashen Turai da kuma Faransa.

Tawagar Congo za ta kara da ko dai ƙasar New Caledonia ko Jamaica a karawar da za yi ta wasannin neman gurbi tsakanin ƙasashen duniya a watan Maris. Wanda ya yi nasara a wasan zai shiga cikin jerin ƙasashe 48 da za su buga gasar kofin duniya, a rukunin K, tare da ƙasashen Portugal da Uzbekistan da kuma Colombia.

 

Hukuncin Da Ake Sa Ran FIFA Za Ta Yanke

Kora: Idan FIFA ta yanke hukuncin cewa dalilan Nijeriya ba su da ƙarfi za ta iya watsi da ƙorafin, ta kuma ƙyale DR Congo ta ci gaba da wasan neman gurbin gasar cin kofin duniya.

Bincike da yin hukunci: FIFA za ta iya yin bincike game da ƙorafin, idan ta gano cewa akwai saɓa ƙa’ida wajen tantance Ƴan wasa, za ta hukunta hukumar (ta hanyar cin tara ko gargaɗi) ba tare da sauya sakamako ba.

Yin hukunci: Idan abin ya yi ƙamari, FIFA ko kuma Hukumar ƙwallon ƙafa ta Afirka za su iya sokewa ko kuma ƙwace maki daga mai laifi a miƙa wa mai ƙorafi ko kuma a cire wa ƙasar maki daga cikin wasannin da aka yi na cikin rukuni. A baya, akan yi wannan hukunci ne idan aka gano ƙarara cewa an take doka, ko dai ta hanyar bayar da bayanan ƙarya ko kuma sauya wasu bayanai.

Duk da cewa Nijeriya ta lashe lambar tagulla a gasar cin kofin Afirka ta 2025, wanda ya sanya ta ƙara ɗabbaƙa kanta a matsayin ɗaya daga cikin ƙasashen da suka gawurta a ɓangaren ƙwallon ƙafa a nahiyar, amma abin da ya fito fili shi ne, a halin yanzu, Nijeriya ba za ta je gasar cin kofin duniya ba, in dai ba wani abu ya sauya ba.

Nijeriya
Abba Ibrahim Wada
+ postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Yadda FIFA Ta Yi Yunƙurin Sasanta Rikicin Israila Da Amurka A Kofin Duniya
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Mece Ce Matsalar Real Madrid? 
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Ko Ka San Dalilin Da Zai Bai Wa Nijeriya Damar Zuwa Gasar Cin Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
Siyasar Kano: Akwai Buƙatar Gwamna Abba Ya Ƙara Nazari

Siyasar Kano: Akwai Buƙatar Gwamna Abba Ya Ƙara Nazari

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.