ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alakar Sin Da EU Na Bukatar Hadin Gwiwa Ba Raba-gari Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
12 months ago
EU

Ko shakka babu kamar yadda alakar sauran kasashen duniya masu karfin tattalin arziki take gudana, Sin da kasashe membobin kungiyar tarayyar Turai ta EU suna da nasu sabani. Amma sabani ba daidai yake da fito-na-fito ba. Hasali na daidai ta hanyar shawarwari ne kadai ake iya warware bambance-bambance, har a kai ga cimma moriyar juna cikin lumana.

Idan mun duba tarihi, za mu ga cewa a bana alakar Sin da EU take cika shekaru 50 da kafuwa, wanda hakan babbar nasara ce da sassan biyu suka cimma, bayan shafe gomman shekaru suna shawarwari, da hadin gwiwa da cimma moriya tare. Tabbas wannan muhimmin lokaci ne na waiwayen baya, da jinjinawa muhimmin kawance na tsawon lokaci dake ci gaba da wanzuwa tsakanin sassan biyu.

  • Anacláudia Rossbach: Ya Kamata Kasashen Afirka Su Koyi Darasi Daga Sin Na Kawar Da Talauci Da Kyautata Kauyuka Zuwa Birane
  • Masu Zuba Jari Na Kasa Da Kasa Sun Gamsu Zuba Jari A Sin Dama Ce Ta Cimma Nasarar More Riba A Nan Gaba

Masharhanta na cewa, duk da sabani a wasu sassa dake bullowa lokaci bayan lokaci tsakanin Sin da EU, a daya bangaren sassan biyu sun more muradun bai daya, musamman gajiyarsu ta fuskar cinikayya, da yaki da sauyin yanayi da jagorancin duniya.

ADVERTISEMENT

A fannin raya cinikayya kuwa, darajar cinikayyar Sin da EU ta karu daga dalar Amurka biliyan 2.4 a shekarar 1975 zuwa kusan dala biliyan 785 a shekarar 2024, ta yadda alakar tattalin arzikinsu ta zamo daya daga mafi karfi, dake ingiza bunkasar tattalin arzikin duniya baki daya. Karkashin hakan, an ga yadda zirga-zirgar jiragen kasa na dakon kaya ke kara habaka tsakanin sassan biyu. A daya bangaren kuma zuba jari domin raya masana’antu tsakanin sassan biyu shi ma ya yi matukar karuwa. An kuma fadada hada-hada a fannonin yawon bude ido, da ilimi, da musaya tsakanin al’ummun Sin da Turai.

A wannan gaba da alakar Sin da Turai ta kai wani muhimmin lokaci a tarihi, kuma sassan biyu ke alfahari da nasarorin da suka cimma, da gajiyar da suke samu a hada-hadar cinikayya, da raya tattalin arziki da sauran muhimman fannoni, abun da ya dace shi ne sassan biyu su kara kwazon aiwatar da matakan yaukaka amincewa da juna, da gina gadar fahimtar juna. Ko shakka babu Sin da EU za su iya cimma wannan nasara, idan sun rungumi ainihin ruhin alakarsu, wato martaba juna, da cimma moriya tare, da kuma raba ribar nasarorin da suke samu. (Saminu Alhassan)

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

EU
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yawan Kwanakin Da Ake Samun Guguwar Rairayi A Kasar Sin Ya Ragu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Hukumomin Kasar Sin Sun Tsara Shirin Kandagarkin Ambaliyar Ruwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya
EU
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”
  • Sulaiman
    Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing
  • Sulaiman
    Yawan Kwanakin Da Ake Samun Guguwar Rairayi A Kasar Sin Ya Ragu
  • Sulaiman
    Hukumomin Kasar Sin Sun Tsara Shirin Kandagarkin Ambaliyar Ruwa

MASU ALAKA

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

July 12, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing
Daga Birnin Sin

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

July 12, 2026
Yawan Kwanakin Da Ake Samun Guguwar Rairayi A Kasar Sin Ya Ragu
Daga Birnin Sin

Yawan Kwanakin Da Ake Samun Guguwar Rairayi A Kasar Sin Ya Ragu

July 12, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kwato Makamai Daga Hannun Ƴan Bindiga, Sun Ceto Yaro A Filato

Sojoji Sun Kwato Makamai Daga Hannun Ƴan Bindiga, Sun Ceto Yaro A Filato

LABARAI MASU NASABA

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

July 12, 2026
FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

July 12, 2026
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

July 12, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

July 12, 2026
Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

July 12, 2026
Yawan Kwanakin Da Ake Samun Guguwar Rairayi A Kasar Sin Ya Ragu

Yawan Kwanakin Da Ake Samun Guguwar Rairayi A Kasar Sin Ya Ragu

July 12, 2026
Hukumomin Kasar Sin Sun Tsara Shirin Kandagarkin Ambaliyar Ruwa

Hukumomin Kasar Sin Sun Tsara Shirin Kandagarkin Ambaliyar Ruwa

July 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.