Wani babban jigo da ke faɗa a ji a zamanin gwamnatin Muhammadu Buhari, Alhaji Lawal Musa Daura ya sauya sheƙa daga jam’iyyar APC zuwa APM mai rogo a Jihar Katsina.
Taron sauya sheƙan ya gudana ne a wani katafaren ɗakin taro mai suna, Monach da ke Jihar Katsina, inda magoya bayansa daga ko’ina su shigo cikin birnin Katsina domin su rufa masa baya.
A lokacin isowar sa, magoya bayansa sun ta ɗaga hannu suna nuna magoya bayansu a gare shi, sun ba da haɗin kai domin hakan zai haifar da ɗa mai ido, wanda ya kasance babban jigo ne a cikin Jihar Katsina da kuma yankin Daura.
Magoya bayan jam’iyyar da dama sun gudanar da jawabai maza da mata wanda daga bisani shi kansa babban jigon ya shiya yi ma jama’a bayanan samun damar sauya sheƙa zuwa sabuwar jam’iyya mai suna APM mai rogo.
A jawabinsa Alhaji Lawal ya bayyana cewa idan har jam’iyyar APM mai rogo ta samu nasara a ƙasar nan, shi ne wanda zai zama mataimakin shugaban ƙasa wanda Mai Girma Oleseyo Abiodun Makinde zai jagoranta.
Tun da farko dai, ya ba jama’a haƙuri bisa shiru da aka ji ya yi a ciki harkokin siyasa, saboda sun gudanar da wasu shirye-shirye, domin Hausawa na ce ja da baya ba tsoro ba ne neman sa’a.
Ya ce sun sauya wannan tafiya domin ci gaban al’ummar ƙasar nan su samu jin daɗi da walwala. Sannan ya yi kira ga magoya bayan jam’iyyar APM a Katsina da Daura da su jajirce wajen ganin haƙarsu ta cimma ruwa.
Ya ce haɗin kai shi ne ke da inganci don ƙarfi ga jam’iyyar da samun sakamako mai inganci da zaman lafiya da ilimi da hanyoyin tallafa wa al’umma da sauran abubuwan ci gaban ƙasar nan.














