Shugaban jam’iyyar NDC na Jihar Kano, Hon. Husaini Isa Mairiga, ya gargaɗi duk ƴan takarar jam’iyyar a kowane mataki da su guji biyan wani kuɗi a cikin wani asusu da ba na uwar jam’iyyar NDC ta ƙasa ko ta ta Jihar Kano ba.
“Duk wanda ya saka kuɗi a wani asusu da ba waɗannan ba, to ya sani ya biya kuɗinsa a banza,” in ji Mairiga a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Kano.
Ya kuma ja hankalin ƴan takarar da ke ganin sun fi ƙarfin jam’iyya, yana mai cewa ranar da hukumar zaɓe ta ƙasa za ta fitar da sunaye ne za su gane cewa “jam’iyya ce uwar kowa.”
“A matsayina na halastaccen shugaban NDC na Kano, duk ɗan takarar da ya ce ba zai bi umarninmu ba, yana ganin ya isa, to za mu buga da shi,” in ji Hon. Mairiga.
Ya ƙara da cewa babu wani ɗan takara da zai karɓi fom ba tare da ya biya kuɗin fom ɗin nuna sha’awa da na ‘nomination’ ba, waɗanda za a miƙa su ga uwar jam’iyya ta ƙasa.
Haka kuma, ya ce wajibi ne kowane ɗan takara ya biya “administratiɓe charges” da “consultation charges” a cikin asusun jam’iyyar NDC na Jihar Kano kaɗai.
Hon. Husaini ya ce idan ba asusun NDC na Kano ba ne, to ka sani ka biya kuɗinka a banza, domin su ne kaɗai aka sani a matsayin halastattun shugabannin jam’iyyar da za su tafi da al’amarin NDC.














