ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amfani Da Bindiga Kawai Ba Zai Magance Matsalar Tsaro Ba – Sheikh Arabi

by Shehu Yahaya
3 years ago
Sheikh Arabi

Shugaban kungiyar Fityanul Islam ta kasa Sheikh Muhammad Arabi Ahmad Abul -Fatahi, ya bayyana cewa amfani da bindiga kadai ba zai magance matsalar tsaron da yayiwa Arewacin Kasar nan katutu mafita ba.

Ya ce.” Bindiga Baza kawo mafita wajen warware matsalar rashin tsaro a Arewa ba har sai mun koma ga koyarwar Annibi Muhammadu (SAW) mu gyara halayenmu wajen tsarkake zukatanmu, kamin zamu iya samun mafita”

  • Muna Bin ‘Yan Bindiga Har Maboyarsu Mu Fatattake Su – Minista
  • Gwamnatin Kano Da ICPC Sun Kulla Alakar Aiki Kan Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

Shugaban ya bayyana haka ne a zantawarsa da wakilinmu jim kadan bayan bude taron majalisar koli na kungiyar fityanu wanda aka gudanar da shi a dakin taro na jami’ar jihar Kaduna.

ADVERTISEMENT

“Matsalar tsaro a Arewa Abune wanda ba boyayyan Abu bane Abu ne wanda kowa yasan halin da Arewacin Nijeriya take ciki musamman a bangaren tsaro muna cikin Hali mawuyaci idan bamuyi hankali ba mu da kanmu zamu war wargaza jihohinmu ko kanmu saboda mafiya yawanmu musulmi ne domin idan kace kashi 80 cikin 100 na Arewacin Nijeriya musulmi ne baka yi laifi ba.

“Mafita shi ne a koma ga Allah Sai halayen al’umma su gyaru, ba zan manta ba a shekarun baya a Arewa lokacin muna matasa a lokacin Ba’a rufe gidajenmu da dare har abinci ake ajiyawa saboda baki, idan bako ya shigo ba Sai ya nemi abinci ba Amma yanzu abin ba haka yake ba”

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Hakazalika, Shehin Malamin ya ce Talauci da rashin aikinyi sune dalilan rashin tsaron.
Sheikh Muhammad Arabi yace Al’umma Suna cikin mawuyacin haii na rashin tsaro da rayuwar kunci inda ya bayyana yunwa da talauci sune silar sace -sace da muyagun ayyuka a Nijeriya.

“Muna kira ga kungiyar gwamnonin Nijeriya da su tabbatar da cewa sun ceto rayuwar al’ummar su saboda ‘Yan Nijeriya suna cikin kuncin rayuwa da rashin zaman lafiya”
Ya kara da cewa ” Muna kira ga Gwamnatin tarayya da ta tabbatar da cewa ta sauke nauyin da ta daukarwa al’ummarta kamin zabe”

Da yake bayani akan iftila’in tashin Bam na Tudun Biri , shugaban ya bayyana gansuwarsa da irin matakin da gwamnatin jihar Kaduna ta dauka yayin faruwar lamarin na Bawa mutanan gudummawar gaggawa.
A kan Hakan ya bukaci gwamnatin tarayya Data tabbatar da ta hukunta wadanda suka kai harin tare da cika alkawarin da gwamnati ta daukarwa al’ummar kasar na kare rayuka da dukiyar al’ummar kasar baki daya.

A jawabin Shugaban Taron Sanata Abu Ibrahim, yace ya zama wajibi al’umma su dage da addu’a domin samun zaman lafiya a Nijeriya.

Ya ce Babu wata gwamnatin da zata goyi Bayan sace -sace da rashin zaman lafiya.
Abu Ibrahim, wanda Sanata Mukhtar Mohammed Dan Dutse ya wakilta, ya taya kungiyar Fityanul Islam murnar cika shekara 60 da kafuwa.

Ya ce “Ganin yadda kungiyar ta dade tana bayar da gudummawa wajen tallafawa addinin musulunci, akwai bukatar a samar da jami’ar musulunci mallakin Fityanul”

Sheikh Arabi
Shehu Yahaya
+ postsBio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamna Uba Sani Ya Yi Jimamin Rasuwar Dan Jarida Jafaru Yakubu Maitama
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamnatin Kaduna Ta Fara Rabon Takin Zamani Kyauta Ga Manoma 150,000
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Zaka Iya Sayar da Takin Gwamnati Ka Sayawa Iyalinka Kaji — Imam Nuradden
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Rashin Tsaro: ACI Zata Kira Taron Gaggawa Na Masu Ruwa Da Tsaki A Kaduna

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Kaya Za Su Kara Tsada Kan Daidaita Farashin Canjin Dala Da CBN Ya Yi Zuwa ₦1,356.883 Kan $1

Kaya Za Su Kara Tsada Kan Daidaita Farashin Canjin Dala Da CBN Ya Yi Zuwa ₦1,356.883 Kan $1

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.