ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amfani Da Bindiga Kawai Ba Zai Magance Matsalar Tsaro Ba – Sheikh Arabi

by Shehu Yahaya
2 years ago
Sheikh Arabi

Shugaban kungiyar Fityanul Islam ta kasa Sheikh Muhammad Arabi Ahmad Abul -Fatahi, ya bayyana cewa amfani da bindiga kadai ba zai magance matsalar tsaron da yayiwa Arewacin Kasar nan katutu mafita ba.

Ya ce.” Bindiga Baza kawo mafita wajen warware matsalar rashin tsaro a Arewa ba har sai mun koma ga koyarwar Annibi Muhammadu (SAW) mu gyara halayenmu wajen tsarkake zukatanmu, kamin zamu iya samun mafita”

  • Muna Bin ‘Yan Bindiga Har Maboyarsu Mu Fatattake Su – Minista
  • Gwamnatin Kano Da ICPC Sun Kulla Alakar Aiki Kan Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

Shugaban ya bayyana haka ne a zantawarsa da wakilinmu jim kadan bayan bude taron majalisar koli na kungiyar fityanu wanda aka gudanar da shi a dakin taro na jami’ar jihar Kaduna.

ADVERTISEMENT

“Matsalar tsaro a Arewa Abune wanda ba boyayyan Abu bane Abu ne wanda kowa yasan halin da Arewacin Nijeriya take ciki musamman a bangaren tsaro muna cikin Hali mawuyaci idan bamuyi hankali ba mu da kanmu zamu war wargaza jihohinmu ko kanmu saboda mafiya yawanmu musulmi ne domin idan kace kashi 80 cikin 100 na Arewacin Nijeriya musulmi ne baka yi laifi ba.

“Mafita shi ne a koma ga Allah Sai halayen al’umma su gyaru, ba zan manta ba a shekarun baya a Arewa lokacin muna matasa a lokacin Ba’a rufe gidajenmu da dare har abinci ake ajiyawa saboda baki, idan bako ya shigo ba Sai ya nemi abinci ba Amma yanzu abin ba haka yake ba”

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Hakazalika, Shehin Malamin ya ce Talauci da rashin aikinyi sune dalilan rashin tsaron.
Sheikh Muhammad Arabi yace Al’umma Suna cikin mawuyacin haii na rashin tsaro da rayuwar kunci inda ya bayyana yunwa da talauci sune silar sace -sace da muyagun ayyuka a Nijeriya.

“Muna kira ga kungiyar gwamnonin Nijeriya da su tabbatar da cewa sun ceto rayuwar al’ummar su saboda ‘Yan Nijeriya suna cikin kuncin rayuwa da rashin zaman lafiya”
Ya kara da cewa ” Muna kira ga Gwamnatin tarayya da ta tabbatar da cewa ta sauke nauyin da ta daukarwa al’ummarta kamin zabe”

Da yake bayani akan iftila’in tashin Bam na Tudun Biri , shugaban ya bayyana gansuwarsa da irin matakin da gwamnatin jihar Kaduna ta dauka yayin faruwar lamarin na Bawa mutanan gudummawar gaggawa.
A kan Hakan ya bukaci gwamnatin tarayya Data tabbatar da ta hukunta wadanda suka kai harin tare da cika alkawarin da gwamnati ta daukarwa al’ummar kasar na kare rayuka da dukiyar al’ummar kasar baki daya.

A jawabin Shugaban Taron Sanata Abu Ibrahim, yace ya zama wajibi al’umma su dage da addu’a domin samun zaman lafiya a Nijeriya.

Ya ce Babu wata gwamnatin da zata goyi Bayan sace -sace da rashin zaman lafiya.
Abu Ibrahim, wanda Sanata Mukhtar Mohammed Dan Dutse ya wakilta, ya taya kungiyar Fityanul Islam murnar cika shekara 60 da kafuwa.

Ya ce “Ganin yadda kungiyar ta dade tana bayar da gudummawa wajen tallafawa addinin musulunci, akwai bukatar a samar da jami’ar musulunci mallakin Fityanul”

Sheikh Arabi
Shehu Yahaya
+ postsBio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Bayan Shehu Sani Ya Ƙalubalanci Zailani, Rikicin APC Ya Ƙara Zafi A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ya Dace ‘Yan Arewa Su Ƙara Marawa Tinubu Baya Domin Kammala Wa’adi Na Biyu — Shehu Sani
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Zargin Ware Ɓangaren El-rufa’i: Rikicin Cikin Gida Ya Kaure A Jam’iyyar ADC, Kaduna

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Kaya Za Su Kara Tsada Kan Daidaita Farashin Canjin Dala Da CBN Ya Yi Zuwa ₦1,356.883 Kan $1

Kaya Za Su Kara Tsada Kan Daidaita Farashin Canjin Dala Da CBN Ya Yi Zuwa ₦1,356.883 Kan $1

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.