ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amfani Da Bindiga Kawai Ba Zai Magance Matsalar Tsaro Ba – Sheikh Arabi

by Shehu Yahaya
2 years ago
Sheikh Arabi

Shugaban kungiyar Fityanul Islam ta kasa Sheikh Muhammad Arabi Ahmad Abul -Fatahi, ya bayyana cewa amfani da bindiga kadai ba zai magance matsalar tsaron da yayiwa Arewacin Kasar nan katutu mafita ba.

Ya ce.” Bindiga Baza kawo mafita wajen warware matsalar rashin tsaro a Arewa ba har sai mun koma ga koyarwar Annibi Muhammadu (SAW) mu gyara halayenmu wajen tsarkake zukatanmu, kamin zamu iya samun mafita”

  • Muna Bin ‘Yan Bindiga Har Maboyarsu Mu Fatattake Su – Minista
  • Gwamnatin Kano Da ICPC Sun Kulla Alakar Aiki Kan Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

Shugaban ya bayyana haka ne a zantawarsa da wakilinmu jim kadan bayan bude taron majalisar koli na kungiyar fityanu wanda aka gudanar da shi a dakin taro na jami’ar jihar Kaduna.

ADVERTISEMENT

“Matsalar tsaro a Arewa Abune wanda ba boyayyan Abu bane Abu ne wanda kowa yasan halin da Arewacin Nijeriya take ciki musamman a bangaren tsaro muna cikin Hali mawuyaci idan bamuyi hankali ba mu da kanmu zamu war wargaza jihohinmu ko kanmu saboda mafiya yawanmu musulmi ne domin idan kace kashi 80 cikin 100 na Arewacin Nijeriya musulmi ne baka yi laifi ba.

“Mafita shi ne a koma ga Allah Sai halayen al’umma su gyaru, ba zan manta ba a shekarun baya a Arewa lokacin muna matasa a lokacin Ba’a rufe gidajenmu da dare har abinci ake ajiyawa saboda baki, idan bako ya shigo ba Sai ya nemi abinci ba Amma yanzu abin ba haka yake ba”

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Hakazalika, Shehin Malamin ya ce Talauci da rashin aikinyi sune dalilan rashin tsaron.
Sheikh Muhammad Arabi yace Al’umma Suna cikin mawuyacin haii na rashin tsaro da rayuwar kunci inda ya bayyana yunwa da talauci sune silar sace -sace da muyagun ayyuka a Nijeriya.

“Muna kira ga kungiyar gwamnonin Nijeriya da su tabbatar da cewa sun ceto rayuwar al’ummar su saboda ‘Yan Nijeriya suna cikin kuncin rayuwa da rashin zaman lafiya”
Ya kara da cewa ” Muna kira ga Gwamnatin tarayya da ta tabbatar da cewa ta sauke nauyin da ta daukarwa al’ummarta kamin zabe”

Da yake bayani akan iftila’in tashin Bam na Tudun Biri , shugaban ya bayyana gansuwarsa da irin matakin da gwamnatin jihar Kaduna ta dauka yayin faruwar lamarin na Bawa mutanan gudummawar gaggawa.
A kan Hakan ya bukaci gwamnatin tarayya Data tabbatar da ta hukunta wadanda suka kai harin tare da cika alkawarin da gwamnati ta daukarwa al’ummar kasar na kare rayuka da dukiyar al’ummar kasar baki daya.

A jawabin Shugaban Taron Sanata Abu Ibrahim, yace ya zama wajibi al’umma su dage da addu’a domin samun zaman lafiya a Nijeriya.

Ya ce Babu wata gwamnatin da zata goyi Bayan sace -sace da rashin zaman lafiya.
Abu Ibrahim, wanda Sanata Mukhtar Mohammed Dan Dutse ya wakilta, ya taya kungiyar Fityanul Islam murnar cika shekara 60 da kafuwa.

Ya ce “Ganin yadda kungiyar ta dade tana bayar da gudummawa wajen tallafawa addinin musulunci, akwai bukatar a samar da jami’ar musulunci mallakin Fityanul”

Sheikh Arabi
Shehu Yahaya
+ postsBio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Bayan Shehu Sani Ya Ƙalubalanci Zailani, Rikicin APC Ya Ƙara Zafi A Kaduna

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Kaya Za Su Kara Tsada Kan Daidaita Farashin Canjin Dala Da CBN Ya Yi Zuwa ₦1,356.883 Kan $1

Kaya Za Su Kara Tsada Kan Daidaita Farashin Canjin Dala Da CBN Ya Yi Zuwa ₦1,356.883 Kan $1

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.