ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amfani Da Bindiga Kawai Ba Zai Magance Matsalar Tsaro Ba – Sheikh Arabi

by Shehu Yahaya
2 years ago
Sheikh Arabi

Shugaban kungiyar Fityanul Islam ta kasa Sheikh Muhammad Arabi Ahmad Abul -Fatahi, ya bayyana cewa amfani da bindiga kadai ba zai magance matsalar tsaron da yayiwa Arewacin Kasar nan katutu mafita ba.

Ya ce.” Bindiga Baza kawo mafita wajen warware matsalar rashin tsaro a Arewa ba har sai mun koma ga koyarwar Annibi Muhammadu (SAW) mu gyara halayenmu wajen tsarkake zukatanmu, kamin zamu iya samun mafita”

  • Muna Bin ‘Yan Bindiga Har Maboyarsu Mu Fatattake Su – Minista
  • Gwamnatin Kano Da ICPC Sun Kulla Alakar Aiki Kan Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

Shugaban ya bayyana haka ne a zantawarsa da wakilinmu jim kadan bayan bude taron majalisar koli na kungiyar fityanu wanda aka gudanar da shi a dakin taro na jami’ar jihar Kaduna.

ADVERTISEMENT

“Matsalar tsaro a Arewa Abune wanda ba boyayyan Abu bane Abu ne wanda kowa yasan halin da Arewacin Nijeriya take ciki musamman a bangaren tsaro muna cikin Hali mawuyaci idan bamuyi hankali ba mu da kanmu zamu war wargaza jihohinmu ko kanmu saboda mafiya yawanmu musulmi ne domin idan kace kashi 80 cikin 100 na Arewacin Nijeriya musulmi ne baka yi laifi ba.

“Mafita shi ne a koma ga Allah Sai halayen al’umma su gyaru, ba zan manta ba a shekarun baya a Arewa lokacin muna matasa a lokacin Ba’a rufe gidajenmu da dare har abinci ake ajiyawa saboda baki, idan bako ya shigo ba Sai ya nemi abinci ba Amma yanzu abin ba haka yake ba”

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Hakazalika, Shehin Malamin ya ce Talauci da rashin aikinyi sune dalilan rashin tsaron.
Sheikh Muhammad Arabi yace Al’umma Suna cikin mawuyacin haii na rashin tsaro da rayuwar kunci inda ya bayyana yunwa da talauci sune silar sace -sace da muyagun ayyuka a Nijeriya.

“Muna kira ga kungiyar gwamnonin Nijeriya da su tabbatar da cewa sun ceto rayuwar al’ummar su saboda ‘Yan Nijeriya suna cikin kuncin rayuwa da rashin zaman lafiya”
Ya kara da cewa ” Muna kira ga Gwamnatin tarayya da ta tabbatar da cewa ta sauke nauyin da ta daukarwa al’ummarta kamin zabe”

Da yake bayani akan iftila’in tashin Bam na Tudun Biri , shugaban ya bayyana gansuwarsa da irin matakin da gwamnatin jihar Kaduna ta dauka yayin faruwar lamarin na Bawa mutanan gudummawar gaggawa.
A kan Hakan ya bukaci gwamnatin tarayya Data tabbatar da ta hukunta wadanda suka kai harin tare da cika alkawarin da gwamnati ta daukarwa al’ummar kasar na kare rayuka da dukiyar al’ummar kasar baki daya.

A jawabin Shugaban Taron Sanata Abu Ibrahim, yace ya zama wajibi al’umma su dage da addu’a domin samun zaman lafiya a Nijeriya.

Ya ce Babu wata gwamnatin da zata goyi Bayan sace -sace da rashin zaman lafiya.
Abu Ibrahim, wanda Sanata Mukhtar Mohammed Dan Dutse ya wakilta, ya taya kungiyar Fityanul Islam murnar cika shekara 60 da kafuwa.

Ya ce “Ganin yadda kungiyar ta dade tana bayar da gudummawa wajen tallafawa addinin musulunci, akwai bukatar a samar da jami’ar musulunci mallakin Fityanul”

Sheikh Arabi
Shehu Yahaya
+ postsBio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje
Labarai

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam
Labarai

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Next Post
Kaya Za Su Kara Tsada Kan Daidaita Farashin Canjin Dala Da CBN Ya Yi Zuwa ₦1,356.883 Kan $1

Kaya Za Su Kara Tsada Kan Daidaita Farashin Canjin Dala Da CBN Ya Yi Zuwa ₦1,356.883 Kan $1

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026
Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)

July 5, 2026
Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Musaya Da Sweden A Dukkanin Fannoni

Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Musaya Da Sweden A Dukkanin Fannoni

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.