Amirul Hajj na jihar Kano kuma Sarkin Gaya, Aliyu Ibrahim Abdulƙadir, ya nuna damuwa kan abin da ya bayyana a matsayin rashin kulawar da Hukumar Alhazai ta Ƙasa, NAHCON, ta yi wa alhazan jihar yayin aikin Hajjin 2026 a ƙasa mai tsarki.
Da yake magana ta bakin mataimakinsa, Sarkin Ƙaraye, Muhammadu Maharaz, Amirul Hajj ya ce alhazan Kano sun fuskanci matsaloli da dama tun daga isowarsu Saudiyya. Ya ce mafi yawan alhazan sun shafe ƙasa da kwana biyu a Madinah maimakon kwanaki hudu ko biyar kamar yadda alhazan wasu jihohi suka samu.
Ya kuma koka kan jinkirin jigilar alhazan Kano zuwa Saudiyya, yana mai cewa hakan ya jefa mutane cikin wahala da damuwa. Haka kuma ya soki ingancin abincin da aka riƙa bai wa alhazai a Madina da Jeddah, yana mai cewa a wasu lokuta ma ba a ba wasu alhazan abinci kwata-kwata ba.
Amirul Hajj ya kuma nuna damuwa kan rashin bai wa wasu alhazai katin Nusuk, wanda ya ce ya hana su gudanar da wasu ibadu cikin sauki. Ya bayyana cewa wasu alhazan sun shafe sama da sa’o’i biyar a cikin motocin bas bayan isa Makkah saboda matsalar katin, lamarin da ya fi shafar mata da tsofaffi.
Da yake mayar da martani, Daraktan Horaswa da Bincike na NAHCON, Abubakar Abubakar Yargawal, ya ba da hakuri kan matsalolin da aka fuskanta tare da tabbatar da cewa hukumar za ta ɗauki matakan gyara domin inganta walwala da jin daɗin alhazan Nijeriya.















Discussion about this post