ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bude Taron Shekara-shekara Na Majalisar Bada Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

An bude zama na biyu na taron majalisar bada shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin wato CPPCC, da wajen karfe 3 na yammacin yau Litinin a birnin Beijing, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping, da sauran jagororin kasar suka halarci zaman bude taron, kuma shugaban majalisar Wang Huning ya gabatar da rahoton aiki a madadin zaunannen kwamitin majalisar ta CPPCC. Rahoton da ta gabatar dai ya waiwayi ayyukan da majalisar ta gudanar a shekara daya da ta gabata, kana ya gabatar da shirin gudanar da ayyukan shekarar bana.

A yayin taron majalisar CPPCC na kwanaki 6, membobin majalisar fiye da dubu biyu, wadanda suka zo daga bangarori 34 za su saurari, tare da dudduba, da kuma tattauna kan rahoton aikin zaunannen kwamitin majalisar ta CPPCC, da rahoton daftarin ayyuka da aka gabatar, kana za su halarci taron shekara-shekara na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin, inda za su saurari, da tattauna rahoton aikin gwamnatin kasar, da bada shawara a fannonin siyasa, da tattalin arziki, da zaman rayuwar jama’a da sauransu.

  • Me Ya Sa Amurka Ke Jin “Tsoron” Kasar Sin Har Da Na’urar Daga Kaya Da Ta Samar?
  • Xi Jinping Ya Taya Shehbaz Sharif Murnar Zama Firaministan Pakistan

Majalisar ba da shawarwari kan harkokin siyasar kasar Sin wato CPPCC, tsari ne dake nuna salon musamman na kasar Sin, kana, muhimmiyar hukuma ce ta hadin-gwiwar jam’iyyu daban-daban gami da gudanar da shawarwarin siyasa a karkashin jagorancin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kuma, muhimmiyar hanya ce da ake bi wajen aiwatar da demokuradiyya daga dukkanin matakai a cikin harkokin siyasar kasar, kuma muhimmin bangare ne a cikin tsarin mulkin kasar.

ADVERTISEMENT

Kwamiti na membobin kasa baki daya na CPPCC, kungiya ce dake aiwatar da tsarin CPPCC, wanda ke kunshe da wakilai daga jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, da sauran jam’iyyun demokuradiyya da ba na kwaminis ba, da wadanda ba sa cikin kowace jam’iyya, da rukunonin al’umma, da wakilai daga kananan kabilu da bangarori daban-daban, da wakilan ‘yan uwanmu daga Taiwan da Hong Kong da Macau, da wakilan Sinawa mazauna kasashen waje da suka dawo da dai sauran wasu bakin da aka ba su goron gayyata na musamman. Manyan ayyukansu su ne, gudanar da shawarwari kan harkokin siyasa, da sa ido bisa tafarkin demokuradiyya, da kuma halartar harkokin siyasa da ba da shawarwari. Wadannan muhimman ayyukan uku sun nuna yadda ‘yan jam’iyyun siyasa gami da kungiyoyi daban-daban, da mutane daga kabilu da bangarori daban-daban suke shiga cikin harkokin kasa, gami da taka muhimmiyar rawarsu a cikin tsarin siyasar kasar Sin, kana, muhimmiyar alama ce dake bambanta majalisar CPPCC da sauran kungiyoyin siyasa.

Shekaru biyar ne wa’adin aikin kowane zagayen ‘yan majalisar CPPCC, kuma a kan gudanar da cikakken zamanta sau daya a kowace shekara. (Zainab Zhang/Murtala Zhang)

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero

Ramadan: Sarkin Kano Ya Roƙi ‘Yan Kasuwa Da Su Taimaka Su Rage Farashin Kayan Abinci

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.