ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Damƙe Wata Yarinya Da Ta Shirya Garkuwa Da Kanta A Edo

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
Edo

Rundunar ƴansandan Jihar Edo ta kama wata yarinya ƴar shekara 18, Obehi Odine, bisa zargin shirya sace kanta da kanta, yayin da aka kuma kama wasu mutum 11 da ake zargin suna da hannu a wata ƙungiyar sace-sace.

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ƴansandan jihar, Eno Ikoedem, ya fitar ranar Talata, ya ce an ƙwato kayayyakin shaida da suka haɗa da makamai a yayin gudanar da ayyukan.

Sanarwar ta ce, “An kama wata da ake kira Obehi Odine  ƴar shekara 18, bisa laifin shirya sace kanta tare da neman kuɗin fansa na Naira miliyan 10.

ADVERTISEMENT
  • Matawalle Na Amafani Da Jami’an Tsaro Don Tsorata ‘Yan Adawa – Kakakin Gwamnan Zamfara 
  • ’Yan Bindiga Sun Kashe Mutum Ɗaya Daga Cikin Likitoci 2 Da Suka Sace A Edo

Ta amsa laifinta, inda ta tabbatar da cewa ta ƙirƙiri lamarin ne da gangan domin damfaro kuɗi.”

A wani aiki mai nasaba da haka a Ubiaja, rundunar ta ce ta samu wata babbar nasara ta hanyar dabarar binciken daji.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

“Baturen ƴansanda na sashen Ubiaja (DPO) da kansa ya jagoranci wani haɗaɗɗen aikin binciken daji a yankin Akwocha Camp da dazukan da ke maƙwabtaka, tare da haɗin gwiwar sojojin Nijeriya da Hukumar Tsaron Jihar Edo (ESSC).

“An kai samame wani wurin ɓoye a cikin daji, wanda rundunar jiragen drone ta gano ta hanyar bayanan sirri daga sa ido ta sama, a matsayin wurin da ake zargin ana amfani da shi wajen sace mutum da ajiyar kayan aiki.”

“Hakan ya kai ga kama mutum 11 maza da ake zargin mambobin wata shiryar ƙungiyar garkuwa da mutum ce mai tsari.

Kayan shaida da aka ƙwato sun haɗa da bindigogin gargajiya guda 24, adda (cutlass) guda 17, gatari na yaƙi guda uku, foda bindiga, fitilun hannu, wayoyin salula, kayan aikin fitila mai amfani da hasken rana, tsafe-tsafe iri-iri, babur guda ɗaya, da kuɗi Naira 209,700, da sauran kayayyaki.”

A halin da ake ciki, Kwamishinan Ƴansanda na jihar, Monday Agbonika, ya gargaɗi jama’a da su guji bayar da rahoton sace-sacen ƙarya ko shiga wasu ayyukan yaudara.

Ya ce irin waɗannan ayyuka na ɓata muhimman kayan aikin tsaro, suna karkatar da hankali daga ainihin gaggawa, suna haifar da firgici ba tare da dalili ba, tare da raunana amincewar jama’a. “Duk wanda aka kama za a gurfanar da shi a gaban doka,” in ji shi.

Agbonika ya sake jaddada aniyar rundunar ta ci gaba da aikin tsaro ta amfani da fasaha, tsauraran matakan mamaye dazuka, da ayyukan tsaro bisa bayanan sirri domin tarwatsa cibiyoyin aikata laifuka a faɗin jihar.

Ya kuma buƙaci jama’a da su ci gaba da bai wa ƴansanda haɗin kai ta hanyar bayar da sahihan bayanai a kan lokaci.

Jaridar The PUNCH ta ruwaito cewa wasu ƴan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutum ne sun nemi kuɗin fansa Naira miliyan 100 domin sakin ƴan Imoga takwas da aka sace a daren Juma’a.

Sarkin Imoga Kingdom, Okpahi na Imoga, Oba Patrick Obajoye, ya bayyana haka a ranar Litinin yayin wata tattaunawa ta wayar tarho.

Ya ce an sace mutumn ne a Star Boy Hotel da ke kan hanyar Imoga–Ibillo a Edo ta Arewa.

Oba Obajoye ya bayyana cewa mutumn sun je Ibillo ne domin wani biki, sannan suka yanke shawarar kwana a Star Boy Hotel, wanda shima mallakin wani ɗan Imoga ne.

Ya ƙara da cewa masu garkuwa da mutumn sun zo otal ɗin sanye da kayan sojoji, suna ɗauke da abin sha, suka yi kamar suna jiran wani ne.

Edo
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
An Kammala Gwaji Na Farko Na Shirye-shiryen Murnar Bikin Sabuwar Shekarar Sinawa Na CMG Na Shekarar 2026

An Kammala Gwaji Na Farko Na Shirye-shiryen Murnar Bikin Sabuwar Shekarar Sinawa Na CMG Na Shekarar 2026

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.