Rundunar ‘Yansandan Nijeriya ta ce ta ceto mutane 309 da aka yi garkuwa da su, tare da kama mutane 129 da ake zargin ‘yan ta’adda ne, a yayin wasu manyan ayyukan tsaro da aka gudanar a jihohin Kogi da Kwara.
An kuma kashe mutane 55 daga cikin waɗanda ake zargi bayan sun ƙi miƙa wuya biyo bayan artabu da jami’an tsaro.
- Kasar Sin Ta Kaddamar Da Wata Manhajar AI Domin Taimakawa Aikin Gona
- ’Yansanda Sun Daƙile Harin ’Yan Bindiga A Ƙauyen Kaduna
Kakakin rundunar ‘yansandan, CSP Benjamin Hundeyin, ya ce mutanen da aka kashe ba a kashe su ta haramtacciyar hanya ba, sai dai sun mutu ne yayin musayar wuta da jami’an tsaro.
Ya bayyana cewa an shafe watanni ana tattara bayanan sirri da tsara aikin kafin a fara shi.
Aikin ya haɗa da rundunonin ‘yansanda daban-daban, sojoji da kuma amfani da jiragen sama, musamman saboda yankunan dajin ne masu wahalar shiga.
Hundeyin ya ce babu wani jami’in tsaro da ya rasa ransa a yayin aikin.
Ya ƙara da cewa aikin tsaron na ci gaba da gudana, kuma jami’an tsaro za su ci gaba da fatattakar ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda a duk wuraren da aka gano suna ɓuya.















Discussion about this post