An gudanar da taron kasa da kasa kan yaki da ta’addanci na shekarar 2026 a birnin Yili na yankin Xinjiang jiya Talata bisa taken “Tunkarar sabbin kalubalen ta’addanci: karfafa sauke nauyin dake wuyan kasa da kasa da kara hadin gwiwarsu”.
Wakilai sama da 100 da suka halarta sun fito ne daga ma’aikatar harkokin waje ta Sin, da sauran hukumomin da abin ya shafa, da gwamnatin yankin Xinjiang, da cibiyoyin masana da jami’o’in Sin, da kasashe 24 da kungiyoyin yanki na kasa da kasa, ciki har da Hadaddiyar Daular Larabawa, da Rasha da AU da dai sauransu.
Bangaren Sin ya nuna cewa, a halin yanzu ayyukan ta’addanci na duniya sun kara kunno kai, kuma nauyin dake bisa wuyan kasashe masu tasowa na yaki da ta’addanci ya karu.
Illar ta’addanci da ta ci gaba da dabaibaye duniya na bullo da matsaloli masu zurfi a cikin tsarin daidaita batun tsaro na duniya. Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarar habaka ci gaban duniya da shawarar inganta tsaron duniya, da shawarar karfafa wayewar kan duniya da kuma shawarar inganta tsarin shugabancin duniya, wadanda suka zama muhimmin jagora wajen fitar da hanyoyin yaki da ta’addanci daga tushe.
Ya kamata al’ummun duniya su nace ga matakan da suka dace don magance matsalolin daga tushe. Kana su aiwatar da tsarin hadin gwiwar kasa da kasa, don tara karfin yaki da ta’addanci.Kazalika, dole ne su karfafa yaki da ta’addanci don cika gibin tsakaninsu a bangaren fasaha, da kuma tsaya tsayin daka kan bin dokar kasa da kasa, ta yadda za a karfafa tushen hadin gwiwarsu.
Bangaren Sin yana fatan raba dabaru da ra’ayoyinsa game da yaki da ta’addanci ga sauran bangarori a karkashin jagorancin manufar samar da kyakkyawar makomar bil’adama ta bai daya, don tinkarar barazanar ta’addanci tare da kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya cikin hadin kai. (Amina Xu)














