A yau Talata ne memban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta Sin kuma ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya gudanar da tattaunawa bisa manyan tsare-tsare tsakanin Sin da Birtaniya karo na 11, tare da babbar jami’ar kula da harkokin wajen Birtaniya Yvette Cooper a nan birnin Beijing.
Yayin tattaunawar, Wang Yi ya bayyana cewa, a matsayinsu na membobin dindindin na kwamitin tsaron MDD, ya kamata Sin da Birtaniya su bayar da jagoranci a fannin bin tsarin dokokin MDD, su tsaya tsayin daka kan ra’ayin cudanyar bangarori daban-daban, tare da inganta gina tsarin shugabanci na duniya mai adalci.
Ya kuma yi karin bayani kan matsayin Sin kan batutuwan Taiwan, da Hong Kong da dai sauransu.
A nata bangare, Cooper ta bayyana cewa, Birtaniya tana son yin aiki tare da Sin, don inganta tattaunawa, ta yadda za a zurfafa hadin gwiwa a fannoni kamar na kasuwanci, da hada-hadar kudi, da makamashi, da fasahar AI da sauyin yanayi. Ta ce Birtaniya tana son ci gaba da aiki tare da Sin ta hanyar tattaunawa bisa gaskiya, da magance bambance-bambance, da kuma inganta ci gaban huldar Birtaniya da Sin cikin kyakkyawan yanayi. (Safiyah Ma)















Discussion about this post