An kaddamar da cibiyar lura da harkokin ‘yan kasa mazauna ketare a birnin Mogadishu fadar mulkin kasar Somaliya, wadda kasar Sin ta bayar da tallafin ginawa. An kaddamar da cibiyar ne a ranar Litinin, kuma ana sa ran za ta taimaka wajen karfafa aiwatar da manufofin Somaliya dangane da ‘yan kasar mazauna ketare, da fadakar da al’ummunta dake kasashen waje, da dinke gudunmawarsu wuri guda don gina kasa.
Firaministan Somaliya Hamza Abdi Barre, da ministan ma’aikatar harkokin waje da hadin gwiwa da kasashen duniya na kasar Abdisalam Abdi Ali, da jakadan kasar Sin a Somaliya Wang Yu ne suka yi hadin gwiwar kaddamar da sabuwar cibiyar mai matsuguni a harabar ma’aikatar harkokin waje da hadin gwiwa da kasashen duniya ta Somaliya.
Da yake tsokaci yayin bikin kaddamarwar, firaminista Barre ya ce sabuwar cibiyar za ta inganta tuntuba tsakanin gwamnati da ‘yan kasar mazauna kasashen waje, tare da taimakawa wajen tsara manufofin kasa masu nasaba da hakan.
A nasa tsokacin kuwa, Ali ya ce karfafa cudanya na da matukar muhimmanci, wajen gina amincewa juna tare da ‘yan kasar mazauna ketare, ya kuma jinjinawa kasar Sin bisa tallafinta wajen gina cibiyar.
Shi kuwa jakadan Sin a Somaliya, Wang Yu cewa ya yi cibiyar ta zamo wata babbar nasara a fannin yaukaka alakar Sin da Somaliya. (Saminu Alhassan)














