Wani jami’in ‘yan ‘sanda mai suna Sani S.O. da ke aiki a ofishin rundunar a Hotoro a Jihar Kano, ya rasu yayin wani rikici tsakanin ‘yan daba, makonni kaɗan kafin ya yi ritaya.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne lokacin da ‘yansanda suka fita domin tarwatsa faɗan da ya ɓarke tsakanin ƙungiyoyin ‘yan daba a yankin.
An ce wani daga cikin ‘yan daban ne ya harbi jami’in da bindiga ƙirar gida a yayin artabun.
An garzaya da shi asibiti, amma likitoci sun tabbatar da rasuwarsa.
Marigayin ya shafe sama da shekaru 30 yana aiki a rundunar ‘yansandan Nijeriya, kuma an bayyana shi a matsayin mutum mai nagarta da ƙima a cikin al’umma.
Ya kusa yin ritaya kafin rasuwarsa.
A ‘yan kwanakin nan rikice-rikicen daba a wasu sassan Kano, ciki har da Hotoro, Fagge, Koki da wasu yankuna sun ta’azzara, musamman yayin da ake tunkarar zaɓen 2027.













Discussion about this post