Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya taya ƙungiyar Arsenal F.C. murnar lashe gasar Firimiyar Ingila bayan shekaru 22.
Atiku, wanda sanannen masoyin Arsenal ne, ya bayyana farin cikinsa a shafinsa na X, inda ya yaba wa ƙungiyar kan jajircewa, haƙuri da haɗin kai da suka nuna har suka samu wannan nasara.
“Ina taya Arsenal murnar lashe gasar Firimiya. Wannan nasara shaida ce ta jajircewa, ladabi da aiki tuƙuru,” in ji Atiku.
Ya ƙara da cewa, “A matsayina na mai goyon bayan Arsenal, yau rana ce ta musamman a gare ni.”
Atiku ya kuma yaba wa ‘yan wasa, masu horarwa da magoya bayan ƙungiyar bisa rawar da suka taka wajen ganin an samu nasarar.
A ƙarshe, ya ce: “Arewacin Landan ya sake zama ja.”















Discussion about this post