ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Nemi Tinubu Ya Taka Wa Gwamna Bago Birki A Kan Cin Zarafin Kafafen Yada Labaru

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
4 months ago
Neja

Kungiyar International Press Institute (IPI) ta yi kira ga Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da ya gargadi Gwamna Mohammed Umar Bago na Jihar Neja kan daukar matakai da za su takura wa ‘yan jarida da kungiyoyin kafofin watsa labarai wajen gudanar da aikinsu na kwararru a jihar.

A cikin wata sanarwa da Fidelis Mbah da Tobi Soniyi, Mataimakin Shugaba da Lauyan IPI Nijeriya suka sanya hannu, kungiyar ta ce wasu daga cikin matakan Gwamna Bago, da kuma na wasu jami’an da ke karkashinsa, sun take ‘yancin ‘yan jarida, inda suka kawo misali da kai farmaki kan Musa Mikail, babban dan jarida na Nigerian Telebision Authority (NTA) a wani taron jama’a a matsayin sabon abin da ya faru.

  • Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Rusa Wata Muhimmiyar Gada A Jihar Neja
  • “Sabon Karfi Mai Samar Da Bunkasuwa” Yana Da Matukar Muhimmanci

An ce Mikail, wanda yake daukar rahoton Iftar na Ramadan a fadar Etsu Nupe a Bida, Jihar Neja a ranar 13 ga Maris, 2026, an tilasta masa barin wurin taron daga wasu masu gadi na musamman bisa umarnin Shehu Abdullahi Maikano, babban jami’in tsaro na Gwamna Bago.

ADVERTISEMENT

A cewarsa ga ma’aikatan NTA, yana tsaye tare da dan kyamararsa lokacin da CSO na Gwamnan ya zo ya tambaye su su matsa.

“Na bayyana cewa ba mu hana kowa ba kuma muna gudanar da aikimmu na kwararru. Duk da haka, ya turani, sauran jami’an tsaro sun kai hari a kaina kuma sun tilasta ni fita daga taron,” in ji Mikail.

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kungiyar IPI ta bayyana cewa farmakin da aka yi wa dan jaridar NTA a baya-bayan nan yana nuna wani mummunan al’amari na take hakkin ‘yan jarida da rashin girmama ‘yancin daukar labarai da Gwamna Bago da wasu jami’an gwamnati ke yi.

Ta tunatar cewa a watan da ya gabata, rundunar ‘yansanda ta Jihar Neja ta kira kuma ta tsare dan jaridar Ahmed Isah Sakpe na Prestige FM, Minna, kan zargin ya bata suna ga jami’in tsaro da ke aiki tare da Gwamna Bago. A watan Nuwamba na bara, Gwamna Bago ya umarci rufe Badeggi FM Radio bisa dalilin yada shirye-shiryen da aka ce sun karfafa mutane su yi adawa da gwamnatinsa.

A watan Mayu, 2025, wani dan jarida mai zaman kansa, Ibrahim Ndamitso, wanda a wani taro ya tambayi Gwamna Bago kan wani sace-sace da ya faru a kan hanyar Kontagora-Minna a watan Oktoba, 2024, an zarge shi da aiki tare da ‘yan fashi, sannan aka mika shi ga ‘yansanda don bincike.

A watan Disamba, 2024, Yakubu Mustapha Bina an kira shi kuma aka yi masa tambayoyi a ofishin SSS na Jihar Neja bayan ya bayar da rahoton cewa tawagar Gwamna Bago ta bace a lokacin yawon zagaye na kauyuka a Yankin Sanata na Arewa-Masu Yamma a ranar 1 Disamba, 2024.

A watan Nuwamba, 2023, Mustapha Batsari, dan jarida na Boice of America (BoA) a Jihar Neja, an kai masa hari kuma an yi masa barazana daga Kwamishinan Tsaron Cikin Gida na Jihar, Manjo Janar Bello Mohammed Abdullahi (ritaya), a cikin Gidan Gwamnati na Minna.

Yunkurin Gwamna Bago da wasu jami’an gwamnatinsa na ci gaba da kokarin hana ‘yan jarida ‘yancin fadar albarkacin baki ya sa an sanya sunansa a cikin Littafin Kunne na IPI Nigeria (Book of Infamy) wanda aka kaddamar a ranar 2 Disamba, 2025, saboda take ‘yancin ‘yan jarida, yi musu barazana, da kokarin hana fadar albarkacin baki.

Dangane da farmakin da aka yi wa babban dan jaridar NTA, IPI Nigeria ta yi kira ga Sufeto Janar na ‘Yansanda, Tunji Disu, da ya gaggauta gudanar da bincike kan lamarin, sannan a hukunta CSO na Gwamna Bago wanda ya ba da umarnin kai farmakin kan dan jaridar.

Haka kuma, IPI ta lissafa Gwamna Bago tare da Gwamna Umoh Eno na Jihar Akwa Ibom da tsohon IGP Kayode Egbetokun, wanda wa’adinsa ya kasance cike da lokuta na tsangwama da farmaki ga ‘yan jarida, a cikin Book of Infamy, wanda Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, ya kaddamar a lokacin taron shekara-shekara da taron gama gari na kungiyar a ranar 2 Disamba, 2025.

Bago
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
Bago
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Next Post
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Kaucewa Takara Mai Hadari

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Kaucewa Takara Mai Hadari

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.