ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Nemi Tinubu Ya Taka Wa Gwamna Bago Birki A Kan Cin Zarafin Kafafen Yada Labaru

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
2 months ago
Neja

Kungiyar International Press Institute (IPI) ta yi kira ga Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da ya gargadi Gwamna Mohammed Umar Bago na Jihar Neja kan daukar matakai da za su takura wa ‘yan jarida da kungiyoyin kafofin watsa labarai wajen gudanar da aikinsu na kwararru a jihar.

A cikin wata sanarwa da Fidelis Mbah da Tobi Soniyi, Mataimakin Shugaba da Lauyan IPI Nijeriya suka sanya hannu, kungiyar ta ce wasu daga cikin matakan Gwamna Bago, da kuma na wasu jami’an da ke karkashinsa, sun take ‘yancin ‘yan jarida, inda suka kawo misali da kai farmaki kan Musa Mikail, babban dan jarida na Nigerian Telebision Authority (NTA) a wani taron jama’a a matsayin sabon abin da ya faru.

  • Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Rusa Wata Muhimmiyar Gada A Jihar Neja
  • “Sabon Karfi Mai Samar Da Bunkasuwa” Yana Da Matukar Muhimmanci

An ce Mikail, wanda yake daukar rahoton Iftar na Ramadan a fadar Etsu Nupe a Bida, Jihar Neja a ranar 13 ga Maris, 2026, an tilasta masa barin wurin taron daga wasu masu gadi na musamman bisa umarnin Shehu Abdullahi Maikano, babban jami’in tsaro na Gwamna Bago.

ADVERTISEMENT

A cewarsa ga ma’aikatan NTA, yana tsaye tare da dan kyamararsa lokacin da CSO na Gwamnan ya zo ya tambaye su su matsa.

“Na bayyana cewa ba mu hana kowa ba kuma muna gudanar da aikimmu na kwararru. Duk da haka, ya turani, sauran jami’an tsaro sun kai hari a kaina kuma sun tilasta ni fita daga taron,” in ji Mikail.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Kungiyar IPI ta bayyana cewa farmakin da aka yi wa dan jaridar NTA a baya-bayan nan yana nuna wani mummunan al’amari na take hakkin ‘yan jarida da rashin girmama ‘yancin daukar labarai da Gwamna Bago da wasu jami’an gwamnati ke yi.

Ta tunatar cewa a watan da ya gabata, rundunar ‘yansanda ta Jihar Neja ta kira kuma ta tsare dan jaridar Ahmed Isah Sakpe na Prestige FM, Minna, kan zargin ya bata suna ga jami’in tsaro da ke aiki tare da Gwamna Bago. A watan Nuwamba na bara, Gwamna Bago ya umarci rufe Badeggi FM Radio bisa dalilin yada shirye-shiryen da aka ce sun karfafa mutane su yi adawa da gwamnatinsa.

A watan Mayu, 2025, wani dan jarida mai zaman kansa, Ibrahim Ndamitso, wanda a wani taro ya tambayi Gwamna Bago kan wani sace-sace da ya faru a kan hanyar Kontagora-Minna a watan Oktoba, 2024, an zarge shi da aiki tare da ‘yan fashi, sannan aka mika shi ga ‘yansanda don bincike.

A watan Disamba, 2024, Yakubu Mustapha Bina an kira shi kuma aka yi masa tambayoyi a ofishin SSS na Jihar Neja bayan ya bayar da rahoton cewa tawagar Gwamna Bago ta bace a lokacin yawon zagaye na kauyuka a Yankin Sanata na Arewa-Masu Yamma a ranar 1 Disamba, 2024.

A watan Nuwamba, 2023, Mustapha Batsari, dan jarida na Boice of America (BoA) a Jihar Neja, an kai masa hari kuma an yi masa barazana daga Kwamishinan Tsaron Cikin Gida na Jihar, Manjo Janar Bello Mohammed Abdullahi (ritaya), a cikin Gidan Gwamnati na Minna.

Yunkurin Gwamna Bago da wasu jami’an gwamnatinsa na ci gaba da kokarin hana ‘yan jarida ‘yancin fadar albarkacin baki ya sa an sanya sunansa a cikin Littafin Kunne na IPI Nigeria (Book of Infamy) wanda aka kaddamar a ranar 2 Disamba, 2025, saboda take ‘yancin ‘yan jarida, yi musu barazana, da kokarin hana fadar albarkacin baki.

Dangane da farmakin da aka yi wa babban dan jaridar NTA, IPI Nigeria ta yi kira ga Sufeto Janar na ‘Yansanda, Tunji Disu, da ya gaggauta gudanar da bincike kan lamarin, sannan a hukunta CSO na Gwamna Bago wanda ya ba da umarnin kai farmakin kan dan jaridar.

Haka kuma, IPI ta lissafa Gwamna Bago tare da Gwamna Umoh Eno na Jihar Akwa Ibom da tsohon IGP Kayode Egbetokun, wanda wa’adinsa ya kasance cike da lokuta na tsangwama da farmaki ga ‘yan jarida, a cikin Book of Infamy, wanda Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, ya kaddamar a lokacin taron shekara-shekara da taron gama gari na kungiyar a ranar 2 Disamba, 2025.

Bago
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya
Bago
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Kaucewa Takara Mai Hadari

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Kaucewa Takara Mai Hadari

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.