ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Wa Dabbobi Sama Da Miliyan Biyar Allurar Rigakafi A Kano

by Abubakar Abba
5 months ago
Dabbobi

A ci gaba da ƙoƙarin da ake yi na ƙara haɓaka fannin kiwon dabbobi a Jihar Kano, Hukumar Kula da Bunƙasa Kiwon Dabbobi ta Jihar Kano, ta yi wa dabbobi sama da miliyan 5.5 allurar rigafin kare su daga kamuwa da cututtuka daban-daban.

A cewar hukumar, ta gudanar da wannan aiki na rigakafin ne a shekaru uku da suka gabata.

Jami’in aikin a jihar, Ibrahim Garba Muhammad ne ya sanar da haka a Kano, wanda ya sanar da cewa; amma tun da farko, hukumar ta tsara za ta yi wa dabbobi miliyan 5.5 ne rigakafin cututtuka daban-daban, inda ya ƙara da cewa; a yanzu haka, ana ci gaba da gudanar da aikin a faɗin jihar.

ADVERTISEMENT
  • An Horas Da Masu Kiwon Dabbobi Dabarun Kiwon Zamani
  • Barkewar Kwalara: Ya Kamata A Dakatar Da Yin Kunu Da Zobo – Karamin Ministan Muhalli

“Ba na jin akwai wata jiha ɗaya a ƙasar nan da za ta iya bugun ƙirje ta ce, ta yi wa dabbobi har kimanin miliyan biyu allurar rigakafin dabbobi a shekaru uku da suka gabata, amma a Jihar Kano an yi hakan, ciki har da kuma zuba jarin sama da naira biliyan ɗaya, domin bayar da horo ga Fulani Makiyaya, don samar da wadatacciyar Madarar Shanu a jihar,” in ji shi.

Muhammad ya ƙara da cewa, KSADP ta kuma samar da asibitin duba lafiyar dabbobi a yankin Danshosiya da ake kiwon dabbobin a zamanance, inda aka keɓe kimanin hekta sama da 2,000, musamman domin a ƙara samar da wadataccen abincin dabbobin.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Ya ci gaba da cewa,  an kuma gyara kusan kimanin hekta 1,000 a yankuna 20, inda aka miƙa su ga ƴan kasuwa a fannin kiwon, domin gudanar da yin sana’ar kiwon.

A cewar tasa, daga cikin ƙoƙarin da KSADP ke yi na ƙara bunƙasa fannin kiwon dabbbobi, musamman domin samun riba da kuma samar musu da kasuwa, inda ya sanar da cewa; an kuma ƙara sabunta aikin kasuwar sarrafa  Fura da Nono da ke   Ƙofar Wambai a jihar ta Kano.

Ya ci gaba da bayyana cewa, an samar da ɗakin adana Mararar Shanu a kasuwar, wanda za a iya adana Madarar sama da 3,000 da hakan zai taimaka wa masu sana’ar tare da ba su damar amfana yadda ya kamata.

Kazalika ya sanar da cewa, an samar da cibibiyon karɓar Madarar Shanu kimanin 98 tare da kammala su da kuma samar musu da na’urorin adana Madarar Shanu kimanin guda 40.

Jami’n ya ci gaba da cewa, sauran cibiyoyin da suka fara gudanar da aikinsu, za su sanya a iya samar da litar Madarar Shanu miliyan 15 a duk shekara, inda ya ƙara da cewa; cibiyoyin za su kuma taimaka wajen samar da sauƙi ga matan Fulani.

Aikin na bunƙasa fannin kiwon na dabbobi da ake gudanarwa a Jihar Kano, Bankin IsDB ya zuba kuɗi da suka kai kimanin dala miliyan 95, musamman don yin kiwon dabbobin, domin samun riba da kuma samar wa da masu sana’ar kasuwa tare da ba su kyakkyawan horo.

Alfanun da aka samu a ƙaraƙashin aikin, ya kai na kimanin naira biliyan 39.2, wanda kuma KSADP ta samar da kayan aiki na zamani tare da samar da shirin bayar da horo da aka samar a shiyoyi uku na Jihar Kano da suka haɗa da Kadawa, Kano ta tsakiya, Ɗanbatta, North da kuma a Gaya ta kudu, inda aka raba wa manoma Taraktocin noma 98 da kuma yin girbin amfanin gona kimanin guda 48.

Dabbobi
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

MASU ALAKA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
Labarai

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya
Rahotonni

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Hukumar Kwastam Ta Fitar Da Wasu Sabbin Ƙa’idoji Ga Kamfanonin Rabar Da Kaya

Hukumar Kwastam Ta Fitar Da Wasu Sabbin Ƙa’idoji Ga Kamfanonin Rabar Da Kaya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.