ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Wa Dabbobi Sama Da Miliyan Biyar Allurar Rigakafi A Kano

by Abubakar Abba
6 months ago
Dabbobi

A ci gaba da ƙoƙarin da ake yi na ƙara haɓaka fannin kiwon dabbobi a Jihar Kano, Hukumar Kula da Bunƙasa Kiwon Dabbobi ta Jihar Kano, ta yi wa dabbobi sama da miliyan 5.5 allurar rigafin kare su daga kamuwa da cututtuka daban-daban.

A cewar hukumar, ta gudanar da wannan aiki na rigakafin ne a shekaru uku da suka gabata.

Jami’in aikin a jihar, Ibrahim Garba Muhammad ne ya sanar da haka a Kano, wanda ya sanar da cewa; amma tun da farko, hukumar ta tsara za ta yi wa dabbobi miliyan 5.5 ne rigakafin cututtuka daban-daban, inda ya ƙara da cewa; a yanzu haka, ana ci gaba da gudanar da aikin a faɗin jihar.

ADVERTISEMENT
  • An Horas Da Masu Kiwon Dabbobi Dabarun Kiwon Zamani
  • Barkewar Kwalara: Ya Kamata A Dakatar Da Yin Kunu Da Zobo – Karamin Ministan Muhalli

“Ba na jin akwai wata jiha ɗaya a ƙasar nan da za ta iya bugun ƙirje ta ce, ta yi wa dabbobi har kimanin miliyan biyu allurar rigakafin dabbobi a shekaru uku da suka gabata, amma a Jihar Kano an yi hakan, ciki har da kuma zuba jarin sama da naira biliyan ɗaya, domin bayar da horo ga Fulani Makiyaya, don samar da wadatacciyar Madarar Shanu a jihar,” in ji shi.

Muhammad ya ƙara da cewa, KSADP ta kuma samar da asibitin duba lafiyar dabbobi a yankin Danshosiya da ake kiwon dabbobin a zamanance, inda aka keɓe kimanin hekta sama da 2,000, musamman domin a ƙara samar da wadataccen abincin dabbobin.

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Ya ci gaba da cewa,  an kuma gyara kusan kimanin hekta 1,000 a yankuna 20, inda aka miƙa su ga ƴan kasuwa a fannin kiwon, domin gudanar da yin sana’ar kiwon.

A cewar tasa, daga cikin ƙoƙarin da KSADP ke yi na ƙara bunƙasa fannin kiwon dabbbobi, musamman domin samun riba da kuma samar musu da kasuwa, inda ya sanar da cewa; an kuma ƙara sabunta aikin kasuwar sarrafa  Fura da Nono da ke   Ƙofar Wambai a jihar ta Kano.

Ya ci gaba da bayyana cewa, an samar da ɗakin adana Mararar Shanu a kasuwar, wanda za a iya adana Madarar sama da 3,000 da hakan zai taimaka wa masu sana’ar tare da ba su damar amfana yadda ya kamata.

Kazalika ya sanar da cewa, an samar da cibibiyon karɓar Madarar Shanu kimanin 98 tare da kammala su da kuma samar musu da na’urorin adana Madarar Shanu kimanin guda 40.

Jami’n ya ci gaba da cewa, sauran cibiyoyin da suka fara gudanar da aikinsu, za su sanya a iya samar da litar Madarar Shanu miliyan 15 a duk shekara, inda ya ƙara da cewa; cibiyoyin za su kuma taimaka wajen samar da sauƙi ga matan Fulani.

Aikin na bunƙasa fannin kiwon na dabbobi da ake gudanarwa a Jihar Kano, Bankin IsDB ya zuba kuɗi da suka kai kimanin dala miliyan 95, musamman don yin kiwon dabbobin, domin samun riba da kuma samar wa da masu sana’ar kasuwa tare da ba su kyakkyawan horo.

Alfanun da aka samu a ƙaraƙashin aikin, ya kai na kimanin naira biliyan 39.2, wanda kuma KSADP ta samar da kayan aiki na zamani tare da samar da shirin bayar da horo da aka samar a shiyoyi uku na Jihar Kano da suka haɗa da Kadawa, Kano ta tsakiya, Ɗanbatta, North da kuma a Gaya ta kudu, inda aka raba wa manoma Taraktocin noma 98 da kuma yin girbin amfanin gona kimanin guda 48.

Dabbobi
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Matatar Ɗangote Ta Ƙaryata Iƙirarin Dillalan Man Fetur 

MASU ALAKA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA
Labarai

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi
Manyan Labarai

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin
Labarai

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026
Next Post
Hukumar Kwastam Ta Fitar Da Wasu Sabbin Ƙa’idoji Ga Kamfanonin Rabar Da Kaya

Hukumar Kwastam Ta Fitar Da Wasu Sabbin Ƙa’idoji Ga Kamfanonin Rabar Da Kaya

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026
Xi Ya Yi Kira Da A Bunkasa Salon Zamanantarwa Na Sin Ta Hanyar Ingiza Kirkire-kirkiren Kimiyya Da Fasaha

Xi Ya Yi Kira Da A Bunkasa Salon Zamanantarwa Na Sin Ta Hanyar Ingiza Kirkire-kirkiren Kimiyya Da Fasaha

July 8, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

July 8, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.