Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Ƙasa NPA, a ƙarƙashin shugannacim Dakta Abubakar Ɗantsoho, ta ƙara ɗaura ɗamarar magance ƙalubalen da ke kawo cikas, a ɓangaren wanzar da samar da sauƙin yin kasuwanci.
Ta ɗauki wannan matakin ne, duba da ƙalubalen da ake samu a hanyoyin shiga da fice a Tashoshin Apapa da Tincan.
Dakta Ɗantsoho ne, ya bayar da wannan tabbacin yayin ganawa da masu ruwa da tsaki a shalkwar NPA, da ke a Marina.
Shugaban ya sanar da cewa, NPA ta yanke shawarar lalubo da mafita, kan waɗanan ƙalubalen, wanda ya ce, tuni, NPA ta gano manyan ƙalubalen kuma za ta magance su.
A cewarsa, matsalolin akasari, sun kasance ne a kan hanyoyin shiga da fita, a Tashoshin Apapa da Tincan, musamman a hanyar zuwa Julius Berger da Oshodi da kuma a kan hanyar Wharf Road zuwa to Ikorodu tare da hanyar Surulere.
Ya ci gaba da cewa, na biyun shi ne wuce iyaka, wanda a tsarin mu, akwai ofishin yansanda da aka kafa domin sanya ido kan hanyoyin shiga da fice, a Tashoshin Ruwan ƙasar.
Kazalika, ya ce, akwai kuma rundunar ƴansanda ta jihar Legas, wanda zai yi wuya, aga ababen hawa na wuce sauran ababen hawa, wanda a wasu lokutan, ake samun tayar da Jijiyar Wuya, a tsakanin masu ababen hawan.
Ya ƙara da cewa, yayin ganawar, masu ruwan da tsaki, sun amince kan hanyoyin da a za a bi, domin yin haɗaka da sauran hukumomin, domin a kawo ƙarshen matsalar.
“Hakan zai kuma magance karɓar cin hanci da daƙile duk wani jinkiri da masu safarar shiga da kaya da fitarwa, a cikin Tashoshin,” Inji Ɗantsoho.
“Tuni mun ɗauki ƙudurin tabbatar da mun samar da kyakyawan yanayi, musamman domin samar da ƙarin walwalar gudanar da hada-hadar kasuwanci a cikin sauƙi wacce kuma ta kai irin mataki na ƙasauran ƙasashen da ke maƙwabtaka da Nijeriya,” A cewar Ɗantsoho.
Shugaban na NPA, ya kuma ƙara nanata ƙudurinsa na ɗaukar dukkan matakan da suka kamata, domin saiat fannin sufurin Jiragen Ruwan ƙasar, duba da cewa, Nijeriya ke kan gaba, a fannin a Afrika da kuma a Afirka ta Tsakiya, wanda hakan ya kuma haura, har zuwa sauran ƙasashe.
A jawabinsa tun da farko Mataimakin Sifeta Janar na ƴansanda da ke kula da zirga-zirgar a Tashoshin Okunade Ronke, ya jaddda buƙaar yin aiki tare da sauran masu ruwa da tsaki a fannin, domin a magance waɗannan ƙalubalen, da ke kawo cikas.
Kan batun wuce ababen hawa ba bisa ƙa’ida ba, mun amince za mu kafa tawagar jami’an tsaro ta musamman a tsakain jihar Legas da masu ruwa da tsaki, domin mu samar da sauƙin yin kasuwancin da kuma samar da kyakyawan yanayi.














