A yau Litinin ne kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya soki lamarin kalaman da firaministar Japan Sanae Takaichi ta furta, dangane da laifukan da kasarta ta aikata na nuna karfin tuwo yayin yakin duniya na biyu, matakin da ya mayar da hannun agogo baya, game da muhimman batutuwan tarihi da suka wakana.
Lin Jian, ya soki firaminista Sanae Takaichi, bisa yadda ta sassauta kamalai game da laifukan da kasarta ta aikata, da mummunar manufar boye gaskiya, da sauya tarihi, da warware matsayar da aka cimma dangane da ayyukan cin zali da Japan din ta aikata.
Lin, ya bayyana hakan ne yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa yau da kullum, lokacin da aka nemi ya yi tsokaci game da furucin Takaichi, cikin jawabinta na ranar kasa ta tunawa da kawo karshen yakin duniya na biyu, wanda Japan din ke bikinta a duk shekara a ranar 15 ga watan Agusta. (Saminu Alhassan)














