ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, September 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Sa Ran Yankin Hong Kong Zai Samu Wani Sabon Ci Gaba A Cikin Shekaru Biyar Masu Zuwa

by CMG Hausa
4 years ago
Hong Kong

LABARAI MASU NASABA

Kamfanonin Kasashen Waje Suna Amfani Da Sabbin Damammakin Bikin CIFTIS

Sin Na Fatan Kiyaye Dokokin Kasa Da Kasa Bisa Yarjejeniyar Sararin Samaniya Tare Da Sauran Kasashe

Tun a lokacin babban taron wakilan jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 18, shugaban kasar Xi Jinping ya nuna kulawa matuka game da wadata da zaman lafiyar yankin musamman na Hong Kong, da moriyar jama’ar wurin da walwalarsu, inda ya yi nuni da cewa, ci gaba shi ne ginshikin raya yankin Hong Kong da kuma magance matsaloli daban-daban.

Shin ta yaya yankin Hong Kong zai samu sabon ci gaba cikin shekaru 5 masu zuwa?
A wajen bikin cika shekaru 25 da dawowar Hong Kong kasar Sin, da kuma bikin rantsar da gwamnati ta shida ta yankin, wanda aka gudanar a jiya Jumma’a, shugaba Xi Jinping ya gabatar da wasu dabaru 4 da yake fatan za su samar da ci gaban HK.

Dabarun hudu sun hada da “Mayar da hankali kan kara matsayin shugabanci” da “Kara karfin inganta ci gaba” da “Warware matsalolin da jama’a ke fuskanta “, da kuma “Wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali tare”.
Xi Jinping ya kuma bayyana fatan sabuwar gwamnatin yankin za ta aiwatar da manufar “kasa daya, mai tsarin mulki biyu” tare da gudanar da ayyuka masu amfani, da kuma mai da hankali kan warware batutuwan da suka fi damun mazauna Hong Kong.

ADVERTISEMENT

Xi Jinping ya bayyana cike da kauna cewa: “A halin yanzu, abin da ya fi jan hankulan jama’ar Hong Kong shi ne, fatan samun rayuwa mafi kyau, da zama a cikin gida mai fadi, da samun karin damammakin raya sana’o’i, da samar da ilimi mai inganci ga yara, da kuma samun kulawa mai inganci idan an tsufa.” Don haka, ya bukaci sabuwar gwamnatin yankin da ta dauki bukatar al’umma, musamman ma fararen hula, a matsayin babbar manufarta ta gudanar da mulki.
Bisa la’akari da yadda ake matukar bukatar tsaro don samun ci gaba, shugaba Xi Jinping ya ce, bayan fuskantar tashin hankali, kowa yana jin cewa, Hong Kong ba zai kasance cikin rudani ba, kuma ba za a iya jinkirta ci gaban yankin ba. Yana mai cewa, dole ne a kawar da duk wani katsalandan tare da mai da hankali kan ci gabansa.” (Mai fassara: Bilkisu Xin)

Hong Kong
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Kamfanonin Kasashen Waje Suna Amfani Da Sabbin Damammakin Bikin CIFTIS
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Suna Amfani Da Sabbin Damammakin Bikin CIFTIS

September 15, 2026
Sin Na Fatan Kiyaye Dokokin Kasa Da Kasa Bisa Yarjejeniyar Sararin Samaniya Tare Da Sauran Kasashe
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Kiyaye Dokokin Kasa Da Kasa Bisa Yarjejeniyar Sararin Samaniya Tare Da Sauran Kasashe

September 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da Zurfafa Hadin Kai A Babban Taron IAEA
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da Zurfafa Hadin Kai A Babban Taron IAEA

September 15, 2026
Next Post
An Gano Sama Da Yara 50 Da Aka Sace A Wani Cocin Ondo

An Gano Sama Da Yara 50 Da Aka Sace A Wani Cocin Ondo

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Katsina

An Raba Keken Adaidaita 238 Domin Kai Marasa Lafiya Asibitoci A Katsina

September 15, 2026
Kamfanonin Kasashen Waje Suna Amfani Da Sabbin Damammakin Bikin CIFTIS

Kamfanonin Kasashen Waje Suna Amfani Da Sabbin Damammakin Bikin CIFTIS

September 15, 2026
Tsoffin Shugabannin Hukumar NFF Sun Bukaci A Nada Kwamitin Watanni 6 Domin Warware Matsalolin Hukumar

Tsoffin Shugabannin Hukumar NFF Sun Bukaci A Nada Kwamitin Watanni 6 Domin Warware Matsalolin Hukumar

September 15, 2026
Sin Na Fatan Kiyaye Dokokin Kasa Da Kasa Bisa Yarjejeniyar Sararin Samaniya Tare Da Sauran Kasashe

Sin Na Fatan Kiyaye Dokokin Kasa Da Kasa Bisa Yarjejeniyar Sararin Samaniya Tare Da Sauran Kasashe

September 15, 2026
NFF Ta Dakatar Da Alkalin Wasa Sakamakon Kwallon Da Ya Hana A Wasan Doma United Da Enyimba

NFF Ta Dakatar Da Alkalin Wasa Sakamakon Kwallon Da Ya Hana A Wasan Doma United Da Enyimba

September 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da Zurfafa Hadin Kai A Babban Taron IAEA

Sin Ta Yi Kira Da Zurfafa Hadin Kai A Babban Taron IAEA

September 15, 2026
'yansanda

Gargaɗi: ‘Yansanda Sun Gano Shirin Kai Hare-hare A Makarantu Da Wuraren Ibada

September 15, 2026
Majalisar Dinkin Duniya Ta Karbi Samfurin Bincike Da Kasar Sin Ta Gudanar A Duniyar Wata  

Majalisar Dinkin Duniya Ta Karbi Samfurin Bincike Da Kasar Sin Ta Gudanar A Duniyar Wata  

September 15, 2026
Dangote

Dalilin Da Ya Sanya Tsadar Man Fetur Ke Ci Gaba Da Shafar Nijeriya — Dangote

September 15, 2026
Xi Ya Bukaci ‘Yan Sandan Sin Su Ci Gaba Da Dukufa Ga Hidimta Wa Jama’a Tare Da Sauke Nauyi Da Nuna Sadaukarwa

Xi Ya Bukaci ‘Yan Sandan Sin Su Ci Gaba Da Dukufa Ga Hidimta Wa Jama’a Tare Da Sauke Nauyi Da Nuna Sadaukarwa

September 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.