Gwamnatin Jihar Katsina ta tabbatar da samun mutane 105 da ake zargin sun kamu da cutar sankarau a ƙananan hukumomi 20 na jihar sakamakon tsananin zafin da ake fama da shi a yankunan.
Babban Daraktan Hukumar Kula da Lafiya a Matakin Farko ta Jihar Katsina, Dakta Shamsuddeen Yahaya ne, ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai a Katsina.
Ya ce har yanzu ana zargin mutanen ne a matsayin masu ɗauke da cutar har sai an tabbatar da ita ta hanyar gwaje-gwaje.
Ya ƙara da cewa duk wanda ya nuna alamomin cutar kamar matsanancin ciwon kai da sankarewar wuya a gaggauta ba shi kulawar lafiya tare da sanya ido a kansa.
Dakta Yahaya ya bayyana cewa wasu ƙananan hukumomi sun fi wasu fuskantar masu alamomin cutar sama da wasu, yana mai cewa gwamnati ta ƙara ƙaimi wajen sa ido da ɗaukar matakan gaggawa domin daƙile yaɗuwar cutar.
Ya kuma bayyana cewa an ƙaddamar da Cibiyar Ayyukan Gaggawa domin haɗa kai da ma’aikatan lafiya wajen aiwatar da matakan daƙile cutar a faɗin jihar.















Discussion about this post