ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC A Zamfara Ta Ayyana Cikakken Goyon Bayanta Ga Tinubu Da Dauda Lawal A Zaɓen 2027

by Sulaiman
1 month ago
Zamfara

Jiga-jigan jam’iyyar APC a Jihar Zamfara sun bayyana cikakken goyon bayansu ga sake zaɓen Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da Gwamna Dauda Lawal a babban zaɓen shekarar 2027.

An bayyana wannan matsaya ne a wani babban taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar da aka gudanar a Gidan Gwamnati da ke Gusau a ranar Asabar, 25 ga Afrilu, 2026.

Taron ya haɗa manyan jiga-jigan APC daga sassa daban-daban na jihar, ciki har da tsofaffin gwamnoni huɗu, zababbun jami’ai, dattawa, wakilan matasa da mata, da sauran masu ruwa da tsaki daga ƙananan hukumomi 14 na jihar.

ADVERTISEMENT

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Lawal ya bayyana cewa lokacin gudanar da irin wannan zama ya dace matuƙa, ganin yadda harkokin siyasa ke ƙara ƙarfi yayin da ake tunkarar zaɓen 2027.

Ya jaddada cewa sauya sheƙar da ya yi zuwa APC ba kawai siyasa ba ce, illa wata dabara ce ta ƙarfafa haɗin gwiwa da Gwamnatin Tarayya domin inganta ci gaban Zamfara.A cewarsa, shirin ceto na “Rescue Mission” da gwamnatinsa ke aiwatarwa na wakiltar muradin al’ummar jihar gaba ɗaya, ba na wata ƙungiya ko ɓangare kaɗai ba. Ya ƙara da cewa gwamnati na mai da hankali wajen dawo da zaman lafiya, gina cibiyoyi, da samar da ayyukan ci gaba da za su amfanar da jama’a.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Gwamnan ya kuma yi kira ga jiga-jigan jam’iyyar da su gudanar da harkokinsu cikin natsuwa da hikima, yana mai jaddada cewa siyasa na buƙatar sulhu, fahimtar juna da kuma yin aiki tare domin cimma manufa.

Ya yi alƙawarin cewa adalci, gaskiya da bin ƙa’ida za su ci gaba da zama ginshiƙai a dukkan matakan tafiyar da jam’iyyar da gwamnati.

A nasu ɓangaren, tsofaffin gwamnoni da suka haɗa da Ahmed Sani Yarima, Mahmud Aliyu Shinkafi, Abdulaziz Yari da kuma Bello Mohammed Matawalle sun tabbatar da cikakken goyon bayansu ga jam’iyyar APC tare da marawa Tinubu da Lawal baya domin sake tsayawa takara a 2027.

Sanarwar taron da Ƙaramin Ministan Tsaro na Ƙasa, Matawalle, ya karanta ta bayyana cewa taron ya ba da dama wajen tattauna muhimman batutuwa da suka shafi haɗin kan jam’iyya, daidaita tafiyar gwamnati, matsalolin tsaro, da kuma shirye-shiryen tunkarar manyan zaɓukan gaba.Taron ya kuma ƙarfafa buƙatar ci gaba da haɗin kai a tsakanin mambobin APC domin tabbatar da nasara a zaɓen 2027, tare da jaddada muhimmancin bin tsarin dimokuraɗiyya na cikin gida da kuma kauce wa duk wani abu da zai kawo rarrabuwar kai.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Harbe-harbe: Trump Da Mataimakinsa Sun Tsallake Rijiya Da Baya A Yayin Babban Taron ‘Yan Jarida

Harbe-harbe: Trump Da Mataimakinsa Sun Tsallake Rijiya Da Baya A Yayin Babban Taron 'Yan Jarida

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.