An shiga firgici a daren Asabar bayan an ji harbe-harbe a wajen taron cin abinci na shekara-shekara na wakilan jaridu masu yaɗa labarai daga gidan Gwamnatin Amurka da ake gudanarwa a birnin Washington, D.C., lamarin da ya haddasa gaggawar matakan tsaro yayin da aka kama wanda ake zargi.
Lamarin ya faru ne a otal ɗin Washington Hilton, inda ɗaruruwan ‘yan jarida, jami’an gwamnati da fitattun mutane suka hallara domin wannan babban taro.

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya halarci taron karo na farko a matsayin shugaban ƙasa tare da uwargidansa, Melania Trump, da Mataimakin Shugaban Ƙasa, JD Vance.
A cewar hukumomi, wani da ake zargin ɗan bindiga ne ya yi ƙoƙarin kutsa kai ta wuraren binciken tsaro da na’urar gano ƙarfe a harabar otal ɗin da misalin ƙarfe 00:45 agogon GMT.
Shaidu sun ce sun ji ƙarar harbe-harbe da dama, wanda ya sa jami’an tsaro na farin kaya na kasar Amurka suka gaggauta fitar da shugaban ƙasar da sauran manyan jami’ai daga wajen taron.
‘Yansanda sun bayyana sunan wanda ake zargin da Cole Tomas Allen, mai shekaru 31 daga gundumar Torrance, California. Shugaban ‘yan sandan Washington, D.C., Jeffery W Carroll, ya ce Allen baƙo ne a otal ɗin, inda ya ƙara da cewa, an riga an killace ɗakinsa domin ci gaba da bincike.
Ana sa ran Allen zai fuskanci tuhume-tuhume da dama, ciki har da amfani da bindiga yayin aikata laifi mai tsanani, lokacin da zai gurfana a kotu gobe Litinin.















Discussion about this post