Reshen jam’iyyar APC a Jihar Bauchi ya bayyana cewa a shirye yake ya karɓi gwamnan jihar, Bala Mohammed, yayin da yake shirin sauya sheƙa daga PDP zuwa APC gabanin zaɓukan 2027.
Mambobin kwamitin APC na jihar ne suka bayyana hakan bayan wata ganawa da gwamnan a gidansa da ke Abuja ranar Laraba, inda suka ce sun tattauna muhimman batutuwa kan yadda sauya sheƙar za ta gudana cikin lumana da fahimta tsakanin ɓangarorin biyu.
- Gwamna Abba Na Ƙoƙarin Jawo Hankalin Shekarau Zuwa APC
- ADC Reshen Kaduna Ta Buƙaci Gwamnati Ta Daina Tsangwamar El-Rufai
Sakataren kwamitin APC na jihar kuma ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Toro, Hon. Dabo Isma’il, ya ce tattaunawar ta mayar da hankali ne kan shirin gwamnan na shiga APC, tare da jaddada buƙatar haɗin kai da bin manufar “Renewed Hope Agenda” ta gwamnatin tarayya.
Ya ƙara da cewa shugabannin jam’iyyar na ƙasa sun buƙaci a marabci gwamnan ba tare da saɓani ba, yana mai cewa an fara tuntuɓa da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da an samu cikakkiyar fahimta kafin sauya sheƙar. Haka kuma ya tabbatar da cewa babu wanda za a nuna wariya ko a zalunta a cikin tsarin.
A nasa ɓangaren, tsohon gwamnan jihar, Isa Yuguda, ya jaddada muhimmancin haɗin kai a cikin jam’iyyar, yana mai cewa nasarar zaɓe ita ce babban buri. Shi ma Hon. Jafaru Leko ya ce za su ci gaba da tuntuɓa domin tabbatar da adalci da daidaito ga dukkan mambobin jam’iyyar yayin da ake ƙara shirin tunkarar zaɓukan gaba.















Discussion about this post