ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai

by Abba Ibrahim Wada
3 days ago
Kofin

Kungiyar kwallon kafa ta Paris Saint-Germain PSG, wadda ita ce za ta kara a kofin, tare da manyan kungiyoyi irin su Manchester City, Aston Billa da Barcelona a matakin league phase na Champions League na wannan kakar.

PSG za ta karbi bakuncin Barcelona a Parc des Princes, sannan kuma ta yi tafiye-tafiye zuwa Billa Park da Manchester domin fuskantar Aston Billa da Manchester City. Kungiyar Arsenal za ta fuskanci Real Madrid da Bayern Munich, Zakarun Premier League Arsenal za su karbi bakuncin Real Madrid a Emirates Stadium, sannan su yi tafiya zuwa Jamus domin karawa da Bayern Munich.

Kungiyar Mikel Arteta za ta kuma kara da Borussia Dortmund, Real Betis, Lille, Napoli, Sabah da Slabia Prague. Manchester City za ta sake haduwa da Rodri da De Bruyne, za ta karbi bakuncin PSG a Etihad Stadium sannan ta yi tafiya zuwa Barcelona, inda za ta kara da tsohon dan wasanta Rodri, wanda ya koma Barcelona a wannan bazarar.

ADVERTISEMENT

Ita kuwa Manchester City kuma za ta fuskanci Napoli, inda za ta sake haduwa da tsohon tauraronta Kebin De Bruyne sai kuma sauran abokan karawarta da suka hada da Sporting CP, Porto, RB Leipzig, AEK Athens da Lens.

Kungiyar kwallon kafa ta Aston Billa wadda ta lashe kofin Europa League ta dawo Champions League za ta karbi bakuncin PSG da Borussia Dortmund, sannan ta yi wasannin waje da Barcelona da Galatasaray. Sauran kungiyoyin da za ta kara da su su ne Club Brugge, Fenerbahce, Biking da Slabia Prague.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

Manchester United ta dawo gasar bayan shekaru biyu za ta kara da Bayern Munich, Atletico Madrid, Roma, Sporting CP, RB Leipzig, Billarreal, Sabah, Como. Sai Liberpool za ta kara da Atletico Madrid da Inter Milan za ta karbi bakuncin, Atletico Madrid, Porto, Billarreal, Lens Sannan za ta yi wasannin waje da Inter Milan, Club Brugge, Fenerbahce, LASK.

Kamar yadda hukumar kwallon kafa ta Eufa ta tsara, za a fara wasannin rukunin matakin farko ne a ranar 8 ga Satumba, yayin da zagayen karshe zai gudana ranar 27 ga Janairu, 2027.

Wadanne Kungiyoyi Ne Za Su Fuskanci Na Premier?

Arsenal: Real Madrid (a gida) Bayern Munich (a waje) Borussia Dortmund (a gida) Real Betis (a waje) Lille (a gida) Napoli (a waje) Sabah (a gida) Slabia Prague (a waje). Aston Billa: PSG (a gida) Barcelona (a waje) Borussia Dortmund (a gida) Club Brugge (a waje) Fenerbahce (a gida) Galatasaray (a waje) Biking (a gida) Slabia Prague (a waje).

Liberpool: Atletico Madrid (a gida) Inter Milan (a waje) Porto (a gida) Club Brugge (a waje) Billarreal (a gida) Fenerbahce (a waje) Lens (a gida) LASK (a waje) Manchester City: PSG (a gida) Barcelona (a waje) Sporting CP (a gida) Porto (a waje) Napoli (a gida) RB Leipzig (a waje) AEK Athens (a gida) Lens (a waje) Manchester United: Bayern Munich (a gida) Atletico Madrid (a waje) Roma (a gida) Sporting CP (a waje) RB Leipzig (a gida) Billarreal (a waje) Sabah (a gida) Como (a waje).

A sabon tsarin Champions League, kowace kungiya daga cikin kungiyoyi 36 za ta buga wasanni takwas da kungiyoyi takwas daban-daban a matakin league phase, inda za ta buga wasanni hudu a gida da hudu a waje. Kungiyoyin da suka kammala a cikin manyan takwas na teburin gasar za su tsallaka kai tsaye zuwa zagayen ‘yan 16. Wadanda suka zo daga matsayi na tara zuwa na 24 kuwa za su buga wasannin neman gurbi gida da waje domin samun damar shiga zagayen ‘yan 16.

Kungiyoyin da suka kammala daga matsayi na 25 zuwa kasa za su fita daga gasar gaba daya, kuma ba za su sauka zuwa gasar Europa League ba. A kakar wasan da ta gabata, Arsenal wadda ta kai wasan karshe ita ce ta zo ta daya a teburin league phase da maki 24 bayan ta yi nasara a dukkan wasanninta takwas.

Liberpool ta zo matsayi na uku da maki 18, bayan Bayern Munich da ta zo ta biyu, yayin da Tottenham ta kammala a matsayi na hudu da maki 17. Chelsea da Manchester City su ma sun tsallaka kai tsaye zuwa zagayen ‘yan 16 bayan sun kammala a matsayi na shida da na takwas bi da bi, yayin da Newcastle ta zo ta 12.

Sai dai Chelsea, Manchester City, Newcastle da Tottenham duk sun fita daga gasar tun a zagayen ‘yan 16 a kakar da ta gabata. Liberpool kuwa PSG ta fitar da ita a wasan kwata-fainal.

Daga baya PSG ta kai wasan karshe inda ta sake doke kungiyar kwallon kafa ta Arsenal, ta kuma lashe kofin Champions League karo na biyu a jere, abin da kungiyar bata taba yi ba.

Kofin
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso
  • Abba Ibrahim Wada
    Ya Manchester City Za Ta Kasance Bayan Tafiyar Guardiola?

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
Mataimakin Firaminista: Sin A Shirye Take Ta Zurfafa Hadin Gwiwar Makamashi A Dukkan Fannoni Da Rasha

Mataimakin Firaminista: Sin A Shirye Take Ta Zurfafa Hadin Gwiwar Makamashi A Dukkan Fannoni Da Rasha

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.