Ɓangaren jam’iyyar PDP da ke ƙarƙashin jagorancin Gwamna Seyi Makinde ya naɗa Barrister Kabiru Tanimu Turaki (SAN) a matsayin Shugaban Kwamitin Rikon Kwarya na Kasa (NWC).
An sanar da naɗin ne a ranar Litinin yayin taron Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) karo na 103 da aka gudanar a Abuja, inda aka amince da Turaki ya jagoranci kwamitin mutane 13 da za su kula da harkokin jam’iyyar na wucin gadi.
Matakin ya biyo bayan ƙudirin da shugaban PDP na jihar Edo, Tony Aziegbemi, ya gabatar, wanda Clement Fagboyede ya mara masa baya, sannan taron ya amince da cikakken jerin sunayen shugabannin rikon kwaryar.
Sauran mambobin kwamitin sun haɗa da Taofeek Arapaja a matsayin Sakatare, tare da Daniel Ambrose, da Hamza Abuya, Ihediwa, da Isah Abubakar, da Theophilus Dakashan, da Ini Ememobong, Aribisala Adewale Idowu, Baru Shaffi da Okechukwu Obiechina.
Ɓangaren PDP na Makinde ya bayyana cewa sabon kwamitin riƙon kwaryar zai jagoranci jam’iyyar tare da tsara matakan da za su daidaita harkokinta a daidai lokacin da ake fuskantar rikicin shugabanci a cikin jam’iyyar.















Discussion about this post