Kyaftin ɗin tawagar ƙwallon ƙafa ta Morocco, Achraf Hakimi, zai gurfana a gaban kotu a Faransa kan zargin aikata fyaɗe.
Rahotanni sun ce matar mai shekaru 24 ta zarge shi da yi mata fyaɗe a gidansa da ke birnin Paris a shekarar 2023.
An fara bincike kan lamarin tun watan Maris na 2023 a yankin Nanterre da ke yammacin Paris.
Alƙalin kotun na Faransa ya umarci a fara shari’ar a watan Fabrairu 2026. Rahotanni sun kuma ce buƙatar Hakimi na a dakatar da ƙarar bai yi nasara ba.
Hakimi, wanda tsohon ɗan wasan Real Madrid ne, ya musanta zargin gaba ɗaya.
Ya ce yana da yaƙini a tsarin shari’a kuma yana fatan a yi masa adalci.
A halin yanzu yana tare da tawagar Morocco a gasar cin kofin duniya, inda za su buga wasanni a Amurka.
Amma akwai yiwuwar samun matsalar zirga-zirga idan Morocco ta kai mataki na gaba, musamman zuwa Kanada ko Mexico saboda dokokin da suka shafi shari’ar.
Hakimi ya shiga jerin ’yan wasa da ke fuskantar irin wannan matsala a ƙwallon ƙafa, kamar yadda aka taɓa hana wasu ’yan wasa shiga wasu ƙasashe saboda shari’o’in da sukw fuskanta.















Discussion about this post